< 詩篇 106 >
1 ヱホバをほめたたへヱホバに感謝せよ そのめぐみはふかくその憐憫はかぎりなし
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 たれかヱホバの力ある事跡をかたり その讃べきことを悉とくいひあらはし得んや
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 審判をまもる人々つねに正義をおこなふ者はさいはひなり
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 ヱホバよなんぢの民にたまふ惠をもて我をおぼえ なんぢの救をもてわれに臨みたまへ
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 さらば我なんぢの撰びたまへる者のさいはひを見 なんぢの國の歓喜をよろこび なんぢの嗣業とともに誇ることをせん
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 われら列祖とともに罪ををかせり 我儕よこしまをなし惡をおこなへり
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 われらの列祖はなんぢがエジプトにてなしたまへる奇しき事跡をさとらず 汝のあはれみの豊かなるを心にとめず 海のほとり即ち紅海のほとりにて逆きたり
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 されどヱホバはその名のゆゑをもて彼等をすくひたまへり こは大なる能力をしらしめんとてなり
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 また紅海を叱咤したまひたれば乾きたり かくて民をみちびきて野をゆくがごとくに淵をすぎしめ
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 恨むるものの手よりかれらをすくひ 仇の手よりかれらを贖ひたまへり
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 水その敵をおほひたればその一人だにのこりし者なかりき
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 このとき彼等そのみことばを信じその頌美をうたへり
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 彼等しばしがほどにその事跡をわすれその訓誨をまたず
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 野にていたくむさぼり荒野にて神をこころみたりき
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 ヱホバはかれらの願欲をかなへたまひしかど その霊魂をやせしめたまへり
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 たみは營のうちにてモーセを嫉みヱホパの聖者アロンをねたみしかば
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 地ひらけてダタンを呑みアビラムの黨類をおほひ
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 火はこのともがらの中にもえおこり熖はあしき者をやきつくせり
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 かれらはホレブの山にて犢をつくり鑄たる像ををがみたり
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 かくの如くおのが榮光をかへて草をくらふ牛のかたちに似す
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 ハムの地にて奇しき事跡をなし紅海のほとりにて懼るべきことを爲たまへり かれは斯る神をわすれたり
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 この故にヱホバかれらを亡さんと宣まへり されど神のえらみたまへる者モーセやぶれの間隙にありてその前にたちその烈怒をひきかへして滅亡をまぬかれしめたり
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 剰さへその幕屋にてつぶやきヱホバの聲をもきかざりき
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 この故に手をあげて彼等にむかひたまへり これ野にてかれらを斃れしめんとし
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 又もろもろの國のうちにてその裔をたふれしめ もろもろの地にかれらを散さんとしたまへるなり
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 彼らはバアルベオルにつきて死るものの祭物をくらひたり
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 斯のごとくその行爲をもてヱホバの烈怒をひきいだしければえやみ侵しいりたり
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 そのときピネハスたちて裁判をなせり かくて疫癘はやみぬ
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 ピネハスは萬代までとこしへにこのことを義とせられたり
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 民メリバの水のほとりにてヱホバの烈怒をひきおこししかば かれらの故によりてモーセも禍害にあへり
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 かれら神の霊にそむきしかばモーセその口唇にて妄にものいひたればなり
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 かれらはヱホバの命じたまへる事にしたがはずしてもろもろの民をほろぼさず
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 反てもろもろの國人とまじりをりてその行爲にならひ
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 罪なき血すなはちカナンの偶像にささげたる己がむすこむすめの血をながしぬ 斯てくには血にてけがされたり
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 またそのわざは自己をけがし そのおこなふところは姦淫なり
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 このゆゑにヱホバの怒その民にむかひて起り その嗣業をにくみて
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 かれらをもろもろの國の手にわたしたまへり 彼等はおのれを恨るものに制へられ
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 おのれの仇にしへたげられ その手の下にうちふせられたり
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 ヱホバはしばしば助けたまひしかどかれらは謀略をまうけて逆き そのよこしまに卑くせられたり
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 されどヱホバはかれらの哭聲をききたまひしとき その患難をかへりみ
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 その契約をかれらの爲におもひいだし その憐憫のゆたかなるにより聖意をかへさせ給ひて
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 かれらを己がとりこにせられたる者どもに憐まるることを得しめたまへり
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 われらの神ヱホバよ われらをすくひて列邦のなかより取集めたまへ われらは聖名に謝し なんぢのほむべき事をほこらん
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 イスラエルの神ヱホバはとこしへより永遠までほむべきかな すべての民はアーメンととなふべし ヱホバを讃稱へよ
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.