< 詩篇 102 >

1 ヱホバよわが祈をききたまへ 願くはわが號呼のこゑの御前にいたらんことを
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 わが窮苦の日みかほを蔽ひたまふなかれ なんぢの耳をわれにかたぶけ 我がよぶ日にすみやかに我にこたへたまへ
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 わがもろもろの日は煙のごとくきえ わが骨はたきぎのごとく焚るるなり
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 わがこころは草のごとく撃れてしほれたり われ糧をくらふを忘れしによる
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 わが歎息のこゑによりてわが骨はわが肉につく
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 われは野の鸅鸕のごとく荒たる跡のふくろふのごとくになりぬ
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 われ醒てねぶらず ただ友なくして屋蓋にをる雀のごとくなれり
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 わが仇はひねもす我をそしる 猖狂ひて我をせむるもの我をさして誓ふ
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 われは糧をくらふごとくに灰をくらひ わが飮ものには涙をまじへたり
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 こは皆なんぢの怒と忿恚とによりてなり なんぢ我をもたげてなげすて給へり
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 わが齡はかたぶける日影のごとし またわれは草のごとく萎れたり
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 されどヱホバよなんぢは永遠にながらへ その名はよろづ世にながらへん
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 なんぢ起てシオンをあはれみたまはん そはシオンに恩惠をほどこしたまふときなり そのさだまれる期すでに來れり
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 なんぢの僕はシオンの石をもよろこび その塵をさへ愛しむ
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 もろもろの國はヱホバの名をおそれ 地のもろもろの王はその榮光をおそれん
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 ヱホバはシオンをきづき榮光をもてあらはれたまへり
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 ヱホバは乏しきものの祈をかへりみ彼等のいのりを藐しめたまはざりき
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 來らんとするのちの世のためにこの事をしるさん 新しくつくられたる民はヤハをほめたたふべし
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 ヱホバその聖所のたかき所よりみおろし天より地をみたまへり
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 こは俘囚のなげきをきき死にさだまれる者をときはなち
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 人々のシオンにてヱホバの名をあらはしヱルサレムにてその頌美をあらはさんが爲なり
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 かかる時にもろもろの民もろもろの國つどひあつまりてヱホバに事へまつらん
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 ヱホバはわがちからを途にておとろへしめ わが齢をみじかからしめ給へり
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 我いへりねがはくはわが神よわがすべての日のなかばにて我をとりさりたまふなかれ 汝のよはひは世々かぎりなし
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 汝いにしへ地の基をすゑたまへり 天もまたなんぢの手の工なり
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 これらは亡びん されど汝はつねに存らへたまはん これらはみな衣のごとくふるびん 汝これらを袍のごとく更たまはん されば彼等はかはらん
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 然れども汝はかはることなし なんぢの齢はをはらざるなり
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 汝のしもべの子輩はながらへん その裔はかたく前にたてらるべし
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< 詩篇 102 >