< ヨブ 記 36 >

1 エリフまた言詞を繼て曰く
Elihu ya ci gaba,
2 暫らく我に容せ我なんぢに示すこと有ん 尚神のために言ふべき事あればなり
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 われ廣くわが知識を取り我の造化主に正義を歸せんとす
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 わが言語は眞實に虚僞ならず 知識の完全き者なんぢの前にあり
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 視よ神は權能ある者にましませども何をも藐視めたまはず その了知の能力は大なり
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 惡しき者を生し存ず 艱難者のために審判を行ひたまふ
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 義しき者に目を離さず 位にある王等とともに永遠に坐せしめて之を貴くしたまふ
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 もし彼ら鏈索に繋がれ 艱難の繩にかかる時は
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 彼らの所行と愆尤とを示してその驕れるを知せ
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 彼らの耳を開きて敎を容れしめ かつ惡を離れて歸れよと彼らに命じたまふ
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 もし彼ら聽したがひて之に事へなば繁昌てその日を送り 樂しくその年を渉らん
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 若かれら聽したがはずば刀劍にて亡び 知識を得ずして死なん
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 しかれども心の邪曲なる者等は忿怒を蓄はへ 神に縛しめらるるとも祈ることを爲ず
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 かれらは年わかくして死亡せ 男娼とその生命をひとしうせん
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 神は艱難者を艱難によりて救ひ 之が耳を虐遇によりて開きたまふ
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 然ば神また汝を狹きところより出して狹からぬ廣き所に移したまふあらん 而して汝の席に陳ぬる物は凡て肥たる物ならん
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 今は惡人の鞫罰なんぢの身に充り 審判と公義となんぢを執ふ
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 なんぢ忿怒に誘はれて嘲笑に陷いらざるやう愼しめよ 收贖の大なるが爲に自ら誤るなかれ
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 なんぢの號叫なんぢを艱難の中より出さんや 如何に力を盡すとも所益あらじ
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 世の人のその處より絶る其夜を慕ふなかれ
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 愼しみて惡に傾むくなかれ 汝は艱難よりも寧ろ之を取んとせり
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 それ神はその權能をもて大なる事を爲したまふ 誰か能く彼のごとくに敎晦を埀んや
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 たれか彼のためにその道を定めし者あらんや 誰かなんぢは惡き事をなせりと言ふことを得ん
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 なんぢ神の御所爲を讚歎ふることを忘れざれ これ世の人の歌ひ崇むる所なり
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 人みな之を仰ぎ觀る 遠き方より人これを視たてまつるなり
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 神は大なる者にいまして我儕かれを知たてまつらず その御年の數は計り知るべからず
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 かれ水を細にして引あげたまへば霧の中に滴り出て雨となるに
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 雲これを降せて人々の上に沛然に灌ぐなり
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 たれか能く雲の舒展る所以 またその幕屋の響く所以を了知んや
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 視よ彼その光明を自己の周圍に繞らし また海の底をも蔽ひたまひ
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 これらをもて民を鞫き また是等をもて食物を豐饒に賜ひ
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 電光をもてその兩手を包み その電光に命じて敵を撃しめたまふ
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 その鳴聲かれを顯はし 家畜すらも彼の來ますを知らすなり
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< ヨブ 記 36 >