< Umarkus 15 >
1 Ani sisizo unu udandang uka tuma wa gurna ahira nigora nan a nanu nan anu nyiti nan nigura, wa tirzizi Yesu wa suru in me, wa ziki me wa nya Bilatus.
Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
2 Bilatus ma iki me, hamani oigome wa Yahudawa/ ma karbirka me, magu wa buka.
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
3 Anu adadandang unyitike wa nan in bi bukum gwardang
Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
4 Bilatus ma kuri ma iki me, ma gun me, ida kuri iboki iri mumba? ira bi bukum me sa ahaza ni anice nuwe me.
Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
5 Yesu da ma kuru ma buki ire imum ba, Bilatus ma diri imumu ubuka.
Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
6 Anyimo atiye ti uru usana, ma meme madi sapi we niteru ni inde, vat uge sa iko.
Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
7 Uru marani agusa me Barnaba, ma tiri ma inde sa wa hirziza muruba, anu wani sa wa huzi anabu anyimo uhirziza umuruba me.
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
8 Ni ori na nabu, ni ha ahira ameme wa ka rizizo me adizi ma gunkune we kasi utanda umeme.
Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
9 Bilatus makabirkawemmagu, inarani in sopi, shi ogomo wa yaduwa me?
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
10 Ma rusa izin iniriba i bit nan anu adadandang u nyetikeme sa wa nya Yesu.
Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
11 In ka ta nya ace ti di cukunu ni gome, a hira imumu iriri i Ugomo Asere.
Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
12 Bilatus ma kabirka we ma kuru magu nyanini idi wuzi ana me. nan Ugomo wa Yahudawa?
Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
13 Wa yeze a nyira magu, ga kirka ni me.
Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
14 Bilatus ma gu we, nyanini ma wu za? wa aje unu kabarsa ume, ga kirka nime.
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
15 Bilatus ma nuari uwuza anabu imumu iriri, ma cekewe Barabas, uganiya sa ma mari ucubo Yesu, ma gu zikani i aka baka me utiti unu rere.
Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
16 Anu uhira uni pin wa ziki me uhana anyimo udange unu dan anipin, wadi titi ni nanu uhira unu pin me.
Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
17 Waduku tiezizi me, upori uvu, waduku barki anice me.
Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
18 Waduku tunguno visisu ume, wa gunme, Asere akinkiwe ti gomoni, Ugomo wa Yahudawa.
Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
19 Waduku dingi vubo ume anice, wa tufizizime tobe, waduku tungunu agi wa zunu nya za ume ti Ugomo.
Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
20 Sa wa mara uzuza ume biranza, waduku sopi upori uvume, waduku suki me ti runga tumeme, wa surin me, amatara uhen uku baka ume utiti uni rere.
Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
21 Uye ma e u aka, niza numeme saminu unanu bakura, acu a Istifanus nan Rufas! a suru ani guro, wa dusa wa busurka me ahi ma ziki utiti uni rere ni Yesu.
Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
22 Wa han in Yesu a ara ahira agusa ani ugolgota, a hira sa a iso nice ni.
Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
23 Waduku nyame ubere agi ma si, ma game usa me.
Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
24 Waduku gakimga tume me wa hari acece awa me, wa wuzi matara aceve awame, wa iri imum besa wadi kenzi.
Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
25 Azumo ukirau udira inde ini sisizo, waduku garkirka me utiti uni rere me.
Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
26 Wa nyetike ihori Asesere utiti uni rere me, wa buki imumu izezen ba ma wuzipa, agi me Ugomo wa Yahudawa.
Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
27 Sa wa gakirka me utiti uni rere me, ana wa re wazi na me, unu inde atari ti na re, unu indw a tari tina agure tumeme.
Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
28 Uganiya uni umyica utize me sa ma buki, a basa ini a nyimo anu wuza uti mumum tizezen.
29 Anu agiza una wa dingi unoo ume tize rizezen, wa haki wa zuri ace, wa gusi, u sa udi u kuri uberla uni anyimo atiye ti tarua.
Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
30 Tuno Asesere utiti uni rere, ubenki nice nuwe me.
sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
31 Ane ani anadandandanh nan anu nyetike utize ta Asere, wa dingi u zunza ume, acece aweme, wa gusi, ma bursa aye, sizikime ubura unice numeme.
Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
32 Unu bursa anu age, Ugomo u Yahudawa ca ma tuu utiti uni rere nigeme a ana me, ti iri haru yi kabi tize ta Asere, a desa agarki kawe nan me we cangi ma zunzi me.
Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
33 Unu wui ace, maree ma impi nipin vat, uhana azumi ataru uwinjoro.
Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
34 Uhana azumo atari Yesu ma hirza ni myiran Asesere magu, Eloi, Eloi Lama Sabatani? agi Asere, Asere nyanini yawuna wa ga mi?
A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
35 Aye wa turi, sa wa kuna ani me, wq gu, ya kuna mazinu tisa Uliya.
Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
36 Uye a nyimo awe, ma sumi maka rumzo nire uni tira in mei ma gwarara, ma tumi ani titi, ma witi Asesere age ma shimbiko, maduku gusi ca tiri nani iliya madi eh ma tuzo me.
Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
37 Yesu ma hirza ni myira Asesere uganiya uduku myinca.
Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
38 Atira anyimo udenge Asere awata tihira kare, uzika Asesere utuno adizi.
Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
39 Uganiya sa vanu uruma uni kara, ma turu mazinu hira u Yesu, ma iri ani me, ma gu, kadura kani unu geme vana Asere mani.
Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
40 Ara ne, wa turu piit wa hiri anyimo, aweme, maryamu magada liya, nan maryamu a ino a Yakubu unu niza ni Yusufu nan Solome.
Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
41 Wa wani a de sa wa tarsi me u ganiya sa mara u Galili wa zin unu wuza ume katuma, nan ane gwardan sa wa igizome Urushalima.
A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
42 Uru winjoro, uwui u bara adudu ani, barki nisizo uwui asabar ani.
Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
43 Yesufu ma eh, unu watu Arimatiya, urunu uka tuma kanipin udadandang, unu nyarga u aye u tize ta Asere, ma wu iriba ihu, ma ribe ahira a Bilatus, ma gu a nyame ikizi Yesu.
Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
44 Bilatus ma basa iriba magu na ma wuu anime, ma titi unu uginome, ma iki me, nani Yesu madodankunu unu wano.
Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
45 Sa ma kuna ani ahira unu dadandang ugino me, ma nya Yusufu ikizi me. Yusufu ma kpe malti, sa ma tuzo iki me nani Yesu madodankunu unu wano.
Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
46 Sa ma kuna ani ahira unu dandang ugino me, ma nya Yusufu ikizi me. Yusufu ma kpe u malti, sa ma tuzo ikizi i Yesu me, ma tirzizi ini umaltime, ma ka suki ini i cau sa a hingir ko nipome acume.
Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
47 Maryamu Magadaliya nan Maryamu a ino a Yusufu wa iri ahira me sa awuna meni.
Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.