< Salmi 78 >

1 Cantico di Asaf. Ascolta, popolo mio, il mio insegnamento; porgete gli orecchi alle parole della mia bocca!
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Io aprirò la mia bocca per proferir parabole, esporrò i misteri de’ tempi antichi.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Quel che noi abbiamo udito e conosciuto, e che i nostri padri ci hanno raccontato,
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 non lo celeremo ai loro figliuoli; diremo alla generazione avvenire le lodi dell’Eterno, e la sua potenza e le maraviglie ch’egli ha operato.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Egli stabilì una testimonianza in Giacobbe, e pose una legge in Israele, ch’egli ordinò ai nostri padri di far conoscere ai loro figliuoli,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 perché fossero note alla generazione avvenire, ai figliuoli che nascerebbero, i quali alla loro volta le narrerebbero ai loro figliuoli,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 ond’essi ponessero in Dio la loro speranza e non dimenticassero le opere di Dio, ma osservassero i suoi comandamenti;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 e non fossero come i loro padri, una generazione caparbia e ribelle, una generazione dal cuore incostante, e il cui spirito non fu fedele a Dio.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 I figliuoli di Efraim, gente di guerra, buoni arcieri, voltaron le spalle il dì della battaglia.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Non osservarono il patto di Dio, e ricusarono di camminar secondo la sua legge;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 e dimenticarono le sue opere e i prodigi ch’egli avea loro fatto vedere.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Egli avea compiuto maraviglie in presenza de’ loro padri, nel paese d’Egitto, nelle campagne di Zoan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Fendé il mare e li fece passare, e fermò le acque come in un mucchio.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Di giorno li guidò con una nuvola, e tutta la notte con una luce di fuoco.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Schiantò rupi nel deserto, e li abbeverò copiosamente, come da gorghi.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Fece scaturire ruscelli dalla roccia e ne fece scender dell’acque a guisa di fiumi.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Ma essi continuarono a peccare contro di lui, a ribellarsi contro l’Altissimo, nel deserto;
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 e tentarono Dio in cuor loro, chiedendo cibo a lor voglia.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 E parlarono contro Dio, dicendo: Potrebbe Dio imbandirci una mensa nel deserto?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Ecco, egli percosse la roccia e ne colarono acque, ne traboccaron torrenti; potrebb’egli darci anche del pane, e provveder di carne il suo popolo?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Perciò l’Eterno, avendoli uditi, s’adirò fieramente, e un fuoco s’accese contro Giacobbe, e l’ira sua si levò contro Israele,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 perché non aveano creduto in Dio, né avevano avuto fiducia nella sua salvazione;
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 eppure egli comandò alle nuvole di sopra, e aprì le porte del cielo,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 e fece piover su loro manna da mangiare, e dette loro del frumento del cielo.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 L’uomo mangiò del pane dei potenti; egli mandò loro del cibo a sazietà.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Fece levare in cielo il vento orientale, e con la sua potenza addusse il vento di mezzodì;
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 fece piover su loro della carne come polvere, degli uccelli alati, numerosi come la rena del mare;
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 e li fece cadere in mezzo al loro campo, d’intorno alle loro tende.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Così essi mangiarono e furon ben satollati, e Dio mandò loro quel che aveano bramato.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Non si erano ancora distolti dalle loro brame, avevano ancora il loro cibo in bocca,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 quando l’ira di Dio si levò contro loro, e ne uccise tra i più fiorenti, e abbatté i giovani d’Israele.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Con tutto ciò peccarono ancora, e non credettero alle sue maraviglie.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Ond’egli consumò i loro giorni in vanità, e i loro anni in ispaventi.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Quand’ei li uccideva, essi lo ricercavano e tornavano bramosi di ritrovare Iddio;
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 e si ricordavano che Dio era la loro ròcca, l’Iddio altissimo il loro redentore.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Essi però lo lusingavano con la loro bocca, e gli mentivano con la loro lingua.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Il loro cuore non era diritto verso lui, e non eran fedeli al suo patto.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Ma egli, che è pietoso, che perdona l’iniquità e non distrugge il peccatore, più volte rattenne la sua ira, e non lasciò divampare tutto il suo cruccio.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Ei si ricordò ch’essi erano carne, un fiato che passa e non ritorna.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Quante volte si ribellarono a lui nel deserto, e lo contristarono nella solitudine!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 E tornarono a tentare Iddio e a provocare il Santo d’Israele.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Non si ricordaron più della sua mano, del giorno in cui egli li liberò dal nemico,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 quando operò i suoi miracoli in Egitto, e i suoi prodigi nelle campagne di Zoan;
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 mutò i loro fiumi in sangue, e i loro rivi in guisa che non potean più bere;
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 mandò contro loro mosche velenose che li divoravano, e rane che li distruggevano;
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 dette il loro raccolto ai bruchi e la loro fatica alle locuste;
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 distrusse le loro vigne con la gragnuola e i loro sicomori coi grossi chicchi d’essa;
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 abbandonò il loro bestiame alla grandine e le lor gregge ai fulmini.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Scatenò su loro l’ardore del suo cruccio, ira, indignazione e distretta, una torma di messaggeri di malanni.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Dette libero corso alla sua ira; non preservò dalla morte la loro anima, ma abbandonò la loro vita alla pestilenza.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Percosse tutti i primogeniti d’Egitto, le primizie del vigore nelle tende di Cham;
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 ma fece partire il suo popolo a guisa di pecore, e lo condusse a traverso il deserto come una mandra.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Lo guidò sicuramente sì che non ebbero da spaventarsi, mentre il mare inghiottiva i loro nemici.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Li fece arrivare alla sua santa frontiera, alla montagna che la sua destra avea conquistato.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Scacciò le nazioni dinanzi a loro, ne assegnò loro a sorte il paese quale eredità, e nelle tende d’esse fece abitare le tribù d’Israele.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 E nondimeno tentarono l’Iddio altissimo e si ribellarono e non osservarono le sue testimonianze.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Si trassero indietro e furono sleali come i loro padri; si rivoltarono come un arco fallace;
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 lo provocarono ad ira coi loro alti luoghi, lo mossero a gelosia con le loro sculture.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Dio udì questo, e si adirò, prese Israele in grande avversione,
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 onde abbandonò il tabernacolo di Silo, la tenda ov’era dimorato fra gli uomini;
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 e lasciò menare la sua Forza in cattività, e lasciò cader la sua Gloria in man del nemico.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Abbandonò il suo popolo alla spada, e s’adirò contro la sua eredità.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Il fuoco consumo i loro giovani, e le loro vergini non ebber canto nuziale.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 I loro sacerdoti caddero per la spada, e le loro vedove non fecer lamento.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Poi il Signore si risvegliò come uno che dormisse, come un prode che grida eccitato dal vino.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 E percosse i suoi nemici alle spalle, e mise loro addosso un eterno vituperio.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Ma ripudiò la tenda di Giuseppe, e non elesse la tribù di Efraim;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 ma elesse la tribù di Giuda, il monte di Sion ch’egli amava.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Edificò il suo santuario a guisa de’ luoghi eccelsi, come la terra ch’egli ha fondata per sempre.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Elesse Davide, suo servitore, lo prese dagli ovili;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 lo trasse di dietro alle pecore lattanti, per pascere Giacobbe suo popolo, ed Israele sua eredità.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Ed egli li pasturò secondo l’integrità del suo cuore, e li guidò con mano assennata.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Salmi 78 >