< Salmi 67 >
1 Salmo di cantico, [dato] al Capo de' Musici, sopra Neghinot IDDIO abbia mercè di noi, e ci benedica; [Iddio] faccia risplendere il suo volto verso noi. (Sela)
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, (Sela)
2 Acciocchè la tua via si conosca in terra, [E] la tua salute fra tutte le genti.
don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.
3 I popoli ti celebreranno, o Dio; I popoli tutti quanti ti celebreranno.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
4 Le nazioni si rallegreranno, e giubileranno; Perciocchè tu giudicherai i popoli dirittamente, E condurrai le nazioni nella terra. (Sela)
Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. (Sela)
5 I popoli ti celebreranno, o Dio; I popoli tutti quanti ti celebreranno.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
6 La terra produrrà il suo frutto; Iddio, l'Iddio nostro ci benedirà.
Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.
7 Iddio ci benedirà; E tutte le estremità della terra lo temeranno.
Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.