< Giobbe 40 >

1 Poi il Signore parlò a Giobbe, e disse:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Colui che litiga con l'Onnipotente[lo] correggerà egli? Colui che arguisce Iddio risponda a questo.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 E Giobbe rispose al Signore, e disse:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Ecco, io sono avvilito; che ti risponderei io? Io metto la mia mano in su la bocca.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 Io ho parlato una volta, ma non replicherò più; Anzi due, ma non continuerò più.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 E il Signore parlò di nuovo a Giobbe dal turbo, e disse:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Cingiti ora i lombi, come un valente uomo; Io ti farò delle domande, e tu insegnami.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Annullerai tu pure il mio giudicio, E mi condannerai tu per giustificarti?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 Hai tu un braccio simile a quel di Dio? O tuoni tu con la voce come egli?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Adornati pur di magnificenza e di altezza; E vestiti di maestà e di gloria.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Spandi i furori dell'ira tua, E riguarda ogni altiero, ed abbassalo;
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Riguarda ogni altiero, ed atterralo; E trita gli empi, e spronfondali;
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Nascondili tutti nella polvere, [E] tura loro la faccia in grotte;
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Allora anch'io ti darò questa lode, Che la tua destra ti può salvare.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Ecco l'ippopotamo, il quale io ho fatto teco; Egli mangia l'erba come il bue.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Ecco, la sua forza [è] ne' lombi, E la sua possa nei muscoli del suo ventre.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Egli rizza la sua coda come un cedro; Ed i nervi delle sue coscie sono intralciati.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Le sue ossa [son come] sbarre di rame, Come mazze di ferro.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 Egli [è] la principale delle opere di Dio; [Sol] colui che l'ha fatto può accostargli la sua spada.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Perchè i monti gli producono il pasco, Tutte le bestie della campagna vi scherzano.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Egli giace sotto gli alberi ombrosi, In ricetti di canne e di paludi.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Gli alberi ombrosi lo coprono [con] l'ombra loro; I salci de' torrenti l'intorniano.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Ecco, egli può far forza ad un fiume, [sì che] non corra; Egli si fida di potersi attrarre il Giordano nella gola.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Prenderallo [alcuno] alla sua vista? Forera[gli] egli il naso, per [mettervi] de' lacci?
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Giobbe 40 >