< Giobbe 26 >
1 E GIOBBE rispose, e disse:
Sai Ayuba ya amsa,
2 O quanto hai tu [bene] aiutato il debole, Ed hai salvato il braccio fiacco!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 O quanto hai tu [ben] consigliato colui che è privo di sapienza, E [gli] hai largamente dimostrata la ragione!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 A cui hai tu tenuti questi ragionamenti? E lo spirito di cui è uscito di te?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 I giganti sono stati formati [da Dio], E [gli animali] che stanno nelle acque [sono stati formati] sotto esse.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 L'inferno [è] ignudo davanti a lui, E non [vi è] copritura alcuna al [luogo del]la perdizione. (Sheol )
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
7 Egli distende l'Aquilone in sul vuoto, Egli tiene sospesa la terra in su niente.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Egli serra le acque nelle sue nuvole, E non però si schiantano le nubi sotto esse.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Egli tavola la superficie del [suo] trono, Egli spande la sua nuvola sopra esso.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Egli ha con la sesta posto un certo termine intorno alle acque, [Il qual durerà] infino alla fine della luce e delle tenebre.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Le colonne de' cieli sono scrollate, Ed attonite, quando egli [le] sgrida.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Egli ha fesso il mare con la sua forza, E col suo senno ha trafitto Rahab.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Egli ha col suo Spirito adorni i cieli; La sua mano ha formato il serpente guizzante.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Ecco, queste cose [son solo] alcune particelle delle sue vie; E quanto poco [è] quel che noi [ne] abbiamo udito? E chi potrà intendere il tuono delle sue potenze?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”