< Salmi 35 >
1 Signore, giudica chi mi accusa, combatti chi mi combatte. Di Davide.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Afferra i tuoi scudi e sorgi in mio aiuto.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Vibra la lancia e la scure contro chi mi insegue, dimmi: «Sono io la tua salvezza».
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Siano confusi e coperti di ignominia quelli che attentano alla mia vita; retrocedano e siano umiliati quelli che tramano la mia sventura.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Siano come pula al vento e l'angelo del Signore li incalzi;
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 la loro strada sia buia e scivolosa quando li insegue l'angelo del Signore.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 Poiché senza motivo mi hanno teso una rete, senza motivo mi hanno scavato una fossa.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Li colga la bufera improvvisa, li catturi la rete che hanno tesa, siano travolti dalla tempesta.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Io invece esulterò nel Signore per la gioia della sua salvezza.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 Tutte le mie ossa dicano: «Chi è come te, Signore, che liberi il debole dal più forte, il misero e il povero dal predatore?».
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Sorgevano testimoni violenti, mi interrogavano su ciò che ignoravo,
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 mi rendevano male per bene: una desolazione per la mia vita.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Io, quand'erano malati, vestivo di sacco, mi affliggevo col digiuno, riecheggiava nel mio petto la mia preghiera.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Mi angustiavo come per l'amico, per il fratello, come in lutto per la madre mi prostravo nel dolore.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 Ma essi godono della mia caduta, si radunano, si radunano contro di me per colpirmi all'improvviso. Mi dilaniano senza posa,
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 mi mettono alla prova, scherno su scherno, contro di me digrignano i denti.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Fino a quando, Signore, starai a guardare? Libera la mia vita dalla loro violenza, dalle zanne dei leoni l'unico mio bene.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 Ti loderò nella grande assemblea, ti celebrerò in mezzo a un popolo numeroso.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Non esultino su di me i nemici bugiardi, non strizzi l'occhio chi mi odia senza motivo.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 Poiché essi non parlano di pace, contro gli umili della terra tramano inganni.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Spalancano contro di me la loro bocca; dicono con scherno: «Abbiamo visto con i nostri occhi!».
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Signore, tu hai visto, non tacere; Dio, da me non stare lontano.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Dèstati, svègliati per il mio giudizio, per la mia causa, Signore mio Dio.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Giudicami secondo la tua giustizia, Signore mio Dio, e di me non abbiano a gioire.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Non pensino in cuor loro: «Siamo soddisfatti!». Non dicano: «Lo abbiamo divorato».
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Sia confuso e svergognato chi gode della mia sventura, sia coperto di vergogna e d'ignominia chi mi insulta.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Esulti e gioisca chi ama il mio diritto, dica sempre: «Grande è il Signore che vuole la pace del suo servo».
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 La mia lingua celebrerà la tua giustizia, canterà la tua lode per sempre.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.