< Salmi 119 >
1 Beato l'uomo di integra condotta, che cammina nella legge del Signore. Alleluia.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Beato chi è fedele ai suoi insegnamenti e lo cerca con tutto il cuore.
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Non commette ingiustizie, cammina per le sue vie.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu hai dato i tuoi precetti perché siano osservati fedelmente.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Siano diritte le mie vie, nel custodire i tuoi decreti.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Allora non dovrò arrossire se avrò obbedito ai tuoi comandi.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Ti loderò con cuore sincero quando avrò appreso le tue giuste sentenze.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Voglio osservare i tuoi decreti: non abbandonarmi mai.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Come potrà un giovane tenere pura la sua via? Custodendo le tue parole.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Con tutto il cuore ti cerco: non farmi deviare dai tuoi precetti.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Conservo nel cuore le tue parole per non offenderti con il peccato.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Benedetto sei tu, Signore; mostrami il tuo volere.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Con le mie labbra ho enumerato tutti i giudizi della tua bocca.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Nel seguire i tuoi ordini è la mia gioia più che in ogni altro bene.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Voglio meditare i tuoi comandamenti, considerare le tue vie.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Nella tua volontà è la mia gioia; mai dimenticherò la tua parola.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Sii buono con il tuo servo e avrò vita, custodirò la tua parola.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Aprimi gli occhi perché io veda le meraviglie della tua legge.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Io sono straniero sulla terra, non nascondermi i tuoi comandi.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Io mi consumo nel desiderio dei tuoi precetti in ogni tempo.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu minacci gli orgogliosi; maledetto chi devìa dai tuoi decreti.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Allontana da me vergogna e disprezzo, perché ho osservato le tue leggi.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Siedono i potenti, mi calunniano, ma il tuo servo medita i tuoi decreti.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Anche i tuoi ordini sono la mia gioia, miei consiglieri i tuoi precetti.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Io sono prostrato nella polvere; dammi vita secondo la tua parola.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Ti ho manifestato le mie vie e mi hai risposto; insegnami i tuoi voleri.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Fammi conoscere la via dei tuoi precetti e mediterò i tuoi prodigi.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Io piango nella tristezza; sollevami secondo la tua promessa.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Tieni lontana da me la via della menzogna, fammi dono della tua legge.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 Ho scelto la via della giustizia, mi sono proposto i tuoi giudizi.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Ho aderito ai tuoi insegnamenti, Signore, che io non resti confuso.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Corro per la via dei tuoi comandamenti, perché hai dilatato il mio cuore.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Indicami, Signore, la via dei tuoi decreti e la seguirò sino alla fine.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Dammi intelligenza, perché io osservi la tua legge e la custodisca con tutto il cuore.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Dirigimi sul sentiero dei tuoi comandi, perché in esso è la mia gioia.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Piega il mio cuore verso i tuoi insegnamenti e non verso la sete del guadagno.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Distogli i miei occhi dalle cose vane, fammi vivere sulla tua via.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Con il tuo servo sii fedele alla parola che hai data, perché ti si tema.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Allontana l'insulto che mi sgomenta, poiché i tuoi giudizi sono buoni.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Ecco, desidero i tuoi comandamenti; per la tua giustizia fammi vivere.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Venga a me, Signore, la tua grazia, la tua salvezza secondo la tua promessa;
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 a chi mi insulta darò una risposta, perché ho fiducia nella tua parola.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Non togliere mai dalla mia bocca la parola vera, perché confido nei tuoi giudizi.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Custodirò la tua legge per sempre, nei secoli, in eterno.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Sarò sicuro nel mio cammino, perché ho ricercato i tuoi voleri.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Davanti ai re parlerò della tua alleanza senza temere la vergogna.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Gioirò per i tuoi comandi che ho amati.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Alzerò le mani ai tuoi precetti che amo, mediterò le tue leggi.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Ricorda la promessa fatta al tuo servo, con la quale mi hai dato speranza.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Questo mi consola nella miseria: la tua parola mi fa vivere.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 I superbi mi insultano aspramente, ma non devìo dalla tua legge.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Ricordo i tuoi giudizi di un tempo, Signore, e ne sono consolato.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 M'ha preso lo sdegno contro gli empi che abbandonano la tua legge.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Sono canti per me i tuoi precetti, nella terra del mio pellegrinaggio.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Ricordo il tuo nome lungo la notte e osservo la tua legge, Signore.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Tutto questo mi accade perché ho custodito i tuoi precetti.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 La mia sorte, ho detto, Signore, è custodire le tue parole.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Con tutto il cuore ti ho supplicato, fammi grazia secondo la tua promessa.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Ho scrutato le mie vie, ho rivolto i miei passi verso i tuoi comandamenti.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Sono pronto e non voglio tardare a custodire i tuoi decreti.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 I lacci degli empi mi hanno avvinto, ma non ho dimenticato la tua legge.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Nel cuore della notte mi alzo a renderti lode per i tuoi giusti decreti.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Sono amico di coloro che ti sono fedeli e osservano i tuoi precetti.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Del tuo amore, Signore, è piena la terra; insegnami il tuo volere.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Hai fatto il bene al tuo servo, Signore, secondo la tua parola.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Insegnami il senno e la saggezza, perché ho fiducia nei tuoi comandamenti.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Prima di essere umiliato andavo errando, ma ora osservo la tua parola.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu sei buono e fai il bene, insegnami i tuoi decreti.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Mi hanno calunniato gli insolenti, ma io con tutto il cuore osservo i tuoi precetti.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Torpido come il grasso è il loro cuore, ma io mi diletto della tua legge.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Bene per me se sono stato umiliato, perché impari ad obbedirti.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 La legge della tua bocca mi è preziosa più di mille pezzi d'oro e d'argento.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Le tue mani mi hanno fatto e plasmato; fammi capire e imparerò i tuoi comandi.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 I tuoi fedeli al vedermi avranno gioia, perché ho sperato nella tua parola.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Signore, so che giusti sono i tuoi giudizi e con ragione mi hai umiliato.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Mi consoli la tua grazia, secondo la tua promessa al tuo servo.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Venga su di me la tua misericordia e avrò vita, poiché la tua legge è la mia gioia.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Siano confusi i superbi che a torto mi opprimono; io mediterò la tua legge.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Si volgano a me i tuoi fedeli e quelli che conoscono i tuoi insegnamenti.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Sia il mio cuore integro nei tuoi precetti, perché non resti confuso.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Mi consumo nell'attesa della tua salvezza, spero nella tua parola.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Si consumano i miei occhi dietro la tua promessa, mentre dico: «Quando mi darai conforto?».
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Io sono come un otre esposto al fumo, ma non dimentico i tuoi insegnamenti.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Quanti saranno i giorni del tuo servo? Quando farai giustizia dei miei persecutori?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Mi hanno scavato fosse gli insolenti che non seguono la tua legge.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Verità sono tutti i tuoi comandi; a torto mi perseguitano: vieni in mio aiuto.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Per poco non mi hanno bandito dalla terra, ma io non ho abbandonato i tuoi precetti.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Secondo il tuo amore fammi vivere e osserverò le parole della tua bocca.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 La tua parola, Signore, è stabile come il cielo.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 La tua fedeltà dura per ogni generazione; hai fondato la terra ed essa è salda.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Per tuo decreto tutto sussiste fino ad oggi, perché ogni cosa è al tuo servizio.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Se la tua legge non fosse la mia gioia, sarei perito nella mia miseria.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Mai dimenticherò i tuoi precetti: per essi mi fai vivere.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Io sono tuo: salvami, perché ho cercato il tuo volere.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Gli empi mi insidiano per rovinarmi, ma io medito i tuoi insegnamenti.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 Di ogni cosa perfetta ho visto il limite, ma la tua legge non ha confini.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 Quanto amo la tua legge, Signore; tutto il giorno la vado meditando.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Il tuo precetto mi fa più saggio dei miei nemici, perché sempre mi accompagna.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Sono più saggio di tutti i miei maestri, perché medito i tuoi insegnamenti.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Ho più senno degli anziani, perché osservo i tuoi precetti.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 Tengo lontano i miei passi da ogni via di male, per custodire la tua parola.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Non mi allontano dai tuoi giudizi, perché sei tu ad istruirmi.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Quanto sono dolci al mio palato le tue parole: più del miele per la mia bocca.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Dai tuoi decreti ricevo intelligenza, per questo odio ogni via di menzogna.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Lampada per i miei passi è la tua parola, luce sul mio cammino.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Ho giurato, e lo confermo, di custodire i tuoi precetti di giustizia.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Sono stanco di soffrire, Signore, dammi vita secondo la tua parola.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Signore, gradisci le offerte delle mie labbra, insegnami i tuoi giudizi.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 La mia vita è sempre in pericolo, ma non dimentico la tua legge.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Gli empi mi hanno teso i loro lacci, ma non ho deviato dai tuoi precetti.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Mia eredità per sempre sono i tuoi insegnamenti, sono essi la gioia del mio cuore.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Ho piegato il mio cuore ai tuoi comandamenti, in essi è la mia ricompensa per sempre.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Detesto gli animi incostanti, io amo la tua legge.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu sei mio rifugio e mio scudo, spero nella tua parola.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Allontanatevi da me o malvagi, osserverò i precetti del mio Dio.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Sostienimi secondo la tua parola e avrò vita, non deludermi nella mia speranza.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Sii tu il mio aiuto e sarò salvo, gioirò sempre nei tuoi precetti.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu disprezzi chi abbandona i tuoi decreti, perché la sua astuzia è fallace.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Consideri scorie tutti gli empi della terra, perciò amo i tuoi insegnamenti.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Tu fai fremere di spavento la mia carne, io temo i tuoi giudizi.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 Ho agito secondo diritto e giustizia; non abbandonarmi ai miei oppressori.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Assicura il bene al tuo servo; non mi opprimano i superbi.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 I miei occhi si consumano nell'attesa della tua salvezza e della tua parola di giustizia.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Agisci con il tuo servo secondo il tuo amore e insegnami i tuoi comandamenti.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Io sono tuo servo, fammi comprendere e conoscerò i tuoi insegnamenti.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 E' tempo che tu agisca, Signore; hanno violato la tua legge.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Perciò amo i tuoi comandamenti più dell'oro, più dell'oro fino.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Per questo tengo cari i tuoi precetti e odio ogni via di menzogna.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Meravigliosa è la tua alleanza, per questo le sono fedele.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 La tua parola nel rivelarsi illumina, dona saggezza ai semplici.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Apro anelante la bocca, perché desidero i tuoi comandamenti.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Volgiti a me e abbi misericordia, tu che sei giusto per chi ama il tuo nome.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Rendi saldi i miei passi secondo la tua parola e su di me non prevalga il male.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Salvami dall'oppressione dell'uomo e obbedirò ai tuoi precetti.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Fà risplendere il volto sul tuo servo e insegnami i tuoi comandamenti.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Fiumi di lacrime mi scendono dagli occhi, perché non osservano la tua legge.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Tu sei giusto, Signore, e retto nei tuoi giudizi.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Con giustizia hai ordinato le tue leggi e con fedeltà grande.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mi divora lo zelo della tua casa, perché i miei nemici dimenticano le tue parole.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Purissima è la tua parola, il tuo servo la predilige.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Io sono piccolo e disprezzato, ma non trascuro i tuoi precetti.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 La tua giustizia è giustizia eterna e verità è la tua legge.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Angoscia e affanno mi hanno colto, ma i tuoi comandi sono la mia gioia.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Giusti sono i tuoi insegnamenti per sempre, fammi comprendere e avrò la vita.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 T'invoco con tutto il cuore, Signore, rispondimi; custodirò i tuoi precetti.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Io ti chiamo, salvami, e seguirò i tuoi insegnamenti.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Precedo l'aurora e grido aiuto, spero sulla tua parola.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 I miei occhi prevengono le veglie per meditare sulle tue promesse.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Ascolta la mia voce, secondo la tua grazia; Signore, fammi vivere secondo il tuo giudizio.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 A tradimento mi assediano i miei persecutori, sono lontani dalla tua legge.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Ma tu, Signore, sei vicino, tutti i tuoi precetti sono veri.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Da tempo conosco le tue testimonianze che hai stabilite per sempre.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Vedi la mia miseria, salvami, perché non ho dimenticato la tua legge.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Difendi la mia causa, riscattami, secondo la tua parola fammi vivere.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Lontano dagli empi è la salvezza, perché non cercano il tuo volere.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Le tue misericordie sono grandi, Signore, secondo i tuoi giudizi fammi vivere.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Sono molti i persecutori che mi assalgono, ma io non abbandono le tue leggi.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Ho visto i ribelli e ne ho provato ribrezzo, perché non custodiscono la tua parola.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Vedi che io amo i tuoi precetti, Signore, secondo la tua grazia dammi vita.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 La verità è principio della tua parola, resta per sempre ogni sentenza della tua giustizia.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 I potenti mi perseguitano senza motivo, ma il mio cuore teme le tue parole.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Io gioisco per la tua promessa, come uno che trova grande tesoro.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Odio il falso e lo detesto, amo la tua legge.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Sette volte al giorno io ti lodo per le sentenze della tua giustizia.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Grande pace per chi ama la tua legge, nel suo cammino non trova inciampo.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Aspetto da te la salvezza, Signore, e obbedisco ai tuoi comandi.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Io custodisco i tuoi insegnamenti e li amo sopra ogni cosa.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Osservo i tuoi decreti e i tuoi insegnamenti: davanti a te sono tutte le mie vie.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Giunga il mio grido fino a te, Signore, fammi comprendere secondo la tua parola.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Venga al tuo volto la mia supplica, salvami secondo la tua promessa.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Scaturisca dalle mie labbra la tua lode, poiché mi insegni i tuoi voleri.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 La mia lingua canti le tue parole, perché sono giusti tutti i tuoi comandamenti.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Mi venga in aiuto la tua mano, poiché ho scelto i tuoi precetti.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Desidero la tua salvezza, Signore, e la tua legge è tutta la mia gioia.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Possa io vivere e darti lode, mi aiutino i tuoi giudizi.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Come pecora smarrita vado errando; cerca il tuo servo, perché non ho dimenticato i tuoi comandamenti.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.