< Giobbe 4 >
1 Elifaz il Temanita prese la parola e disse:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Se si tenta di parlarti, ti sarà forse gravoso? Ma chi può trattenere il discorso?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Ecco, tu hai istruito molti e a mani fiacche hai ridato vigore;
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 le tue parole hanno sorretto chi vacillava e le ginocchia che si piegavano hai rafforzato.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Ma ora questo accade a te e ti abbatti; capita a te e ne sei sconvolto.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 La tua pietà non era forse la tua fiducia e la tua condotta integra, la tua speranza?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Ricordalo: quale innocente è mai perito e quando mai furon distrutti gli uomini retti?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 Per quanto io ho visto, chi coltiva iniquità, chi semina affanni, li raccoglie.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 A un soffio di Dio periscono e dallo sfogo della sua ira sono annientati.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 Il ruggito del leone e l'urlo del leopardo e i denti dei leoncelli sono frantumati.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 Il leone è perito per mancanza di preda e i figli della leonessa sono stati dispersi.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 A me fu recata, furtiva, una parola e il mio orecchio ne percepì il lieve sussurro.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 Nei fantasmi, tra visioni notturne, quando grava sugli uomini il sonno,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 terrore mi prese e spavento e tutte le ossa mi fece tremare;
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 un vento mi passò sulla faccia, e il pelo si drizzò sulla mia carne...
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Stava là ritto uno, di cui non riconobbi l'aspetto, un fantasma stava davanti ai miei occhi... Un sussurro..., e una voce mi si fece sentire:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 «Può il mortale essere giusto davanti a Dio o innocente l'uomo davanti al suo creatore?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Ecco, dei suoi servi egli non si fida e ai suoi angeli imputa difetti;
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 quanto più a chi abita case di fango, che nella polvere hanno il loro fondamento! Come tarlo sono schiacciati,
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 annientati fra il mattino e la sera: senza che nessuno ci badi, periscono per sempre.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 La funicella della loro tenda non viene forse strappata? Muoiono senza saggezza!».
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’