< Giobbe 19 >
2 Fino a quando mi tormenterete e mi opprimerete con le vostre parole?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Son dieci volte che mi insultate e mi maltrattate senza pudore.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 E' poi vero che io abbia mancato e che persista nel mio errore?
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Non è forse vero che credete di vincere contro di me, rinfacciandomi la mia abiezione?
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Sappiate dunque che Dio mi ha piegato e mi ha avviluppato nella sua rete.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Ecco, grido contro la violenza, ma non ho risposta, chiedo aiuto, ma non c'è giustizia!
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Mi ha sbarrato la strada perché non passi e sul mio sentiero ha disteso le tenebre.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Mi ha spogliato della mia gloria e mi ha tolto dal capo la corona.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 Mi ha disfatto da ogni parte e io sparisco, mi ha strappato, come un albero, la speranza.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 Ha acceso contro di me la sua ira e mi considera come suo nemico.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Insieme sono accorse le sue schiere e si sono spianata la strada contro di me; hanno posto l'assedio intorno alla mia tenda.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 I miei fratelli si sono allontanati da me, persino gli amici mi si sono fatti stranieri.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 Scomparsi sono vicini e conoscenti, mi hanno dimenticato gli ospiti di casa;
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 da estraneo mi trattano le mie ancelle, un forestiero sono ai loro occhi.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 Chiamo il mio servo ed egli non risponde, devo supplicarlo con la mia bocca.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 Il mio fiato è ripugnante per mia moglie e faccio schifo ai figli di mia madre.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Anche i monelli hanno ribrezzo di me: se tento d'alzarmi, mi danno la baia.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Mi hanno in orrore tutti i miei confidenti: quelli che amavo si rivoltano contro di me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Alla pelle si attaccano le mie ossa e non è salva che la pelle dei miei denti.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Pietà, pietà di me, almeno voi miei amici, perché la mano di Dio mi ha percosso!
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Perché vi accanite contro di me, come Dio, e non siete mai sazi della mia carne?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Oh, se le mie parole si scrivessero, se si fissassero in un libro,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 fossero impresse con stilo di ferro sul piombo, per sempre s'incidessero sulla roccia!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Io lo so che il mio Vendicatore è vivo e che, ultimo, si ergerà sulla polvere!
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 Dopo che questa mia pelle sarà distrutta, senza la mia carne, vedrò Dio.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Io lo vedrò, io stesso, e i miei occhi lo contempleranno non da straniero. Le mie viscere si consumano dentro di me.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Poiché dite: «Come lo perseguitiamo noi, se la radice del suo danno è in lui?»,
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 temete per voi la spada, poiché punitrice d'iniquità è la spada, affinchè sappiate che c'è un giudice.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”