< Giobbe 18 >
1 Bildad il Suchita prese a dire:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Quando porrai fine alle tue chiacchiere? Rifletti bene e poi parleremo.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Perché considerarci come bestie, ci fai passare per bruti ai tuoi occhi?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Tu che ti rodi l'anima nel tuo furore, forse per causa tua sarà abbandonata la terra e le rupi si staccheranno dal loro posto?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Certamente la luce del malvagio si spegnerà e più non brillerà la fiamma del suo focolare.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 La luce si offuscherà nella sua tenda e la lucerna si estinguerà sopra di lui.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Il suo energico passo s'accorcerà e i suoi progetti lo faran precipitare,
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 poiché incapperà in una rete con i suoi piedi e sopra un tranello camminerà.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Un laccio l'afferrerà per il calcagno, un nodo scorsoio lo stringerà.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Gli è nascosta per terra una fune e gli è tesa una trappola sul sentiero.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Lo spaventano da tutte le parti terrori e lo inseguono alle calcagna.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Diventerà carestia la sua opulenza e la rovina è lì in piedi al suo fianco.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Un malanno divorerà la sua pelle, roderà le sue membra il primogenito della morte.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Sarà tolto dalla tenda in cui fidava, per essere trascinato al re dei terrori!
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Potresti abitare nella tenda che non è più sua; sulla sua dimora si spargerà zolfo.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Al di sotto, le sue radici si seccheranno, sopra, saranno tagliati i suoi rami.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Il suo ricordo sparirà dalla terra e il suo nome più non si udrà per la contrada.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Lo getteranno dalla luce nel buio e dal mondo lo stermineranno.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Non famiglia, non discendenza avrà nel suo popolo, non superstiti nei luoghi della sua dimora.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Della sua fine stupirà l'occidente e l'oriente ne prenderà orrore.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Ecco qual è la sorte dell'iniquo: questa è la dimora di chi misconosce Dio.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”