< Genesi 11 >

1 Tutta la terra aveva una sola lingua e le stesse parole.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 Emigrando dall'oriente gli uomini capitarono in una pianura nel paese di Sennaar e vi si stabilirono.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 Si dissero l'un l'altro: «Venite, facciamoci mattoni e cuociamoli al fuoco». Il mattone servì loro da pietra e il bitume da cemento.
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 Poi dissero: «Venite, costruiamoci una città e una torre, la cui cima tocchi il cielo e facciamoci un nome, per non disperderci su tutta la terra».
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 Ma il Signore scese a vedere la città e la torre che gli uomini stavano costruendo.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 Il Signore disse: «Ecco, essi sono un solo popolo e hanno tutti una lingua sola; questo è l'inizio della loro opera e ora quanto avranno in progetto di fare non sarà loro impossibile.
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 Scendiamo dunque e confondiamo la loro lingua, perché non comprendano più l'uno la lingua dell'altro».
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 Il Signore li disperse di là su tutta la terra ed essi essarono di costruire la città.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 Per questo la si chiamò Babele, perché là il Signore confuse la lingua di tutta la terra e di là il Signore li disperse su tutta la terra.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 Questa è la discendenza di Sem: Sem aveva cento anni quando generò Arpacsad, due anni dopo il diluvio;
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 Sem, dopo aver generato Arpacsad, visse cinquecento anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 Arpacsad aveva trentacinque anni quando generò Selach;
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 Arpacsad, dopo aver generato Selach, visse quattrocentotrè anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 Selach aveva trent'anni quando generò Eber;
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 Selach, dopo aver generato Eber, visse quattrocentotrè anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 Eber aveva trentaquattro anni quando generò Peleg;
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 Eber, dopo aver generato Peleg, visse quattrocentotrenta anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 Peleg aveva trent'anni quando generò Reu;
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 Peleg, dopo aver generato Reu, visse duecentonove anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 Reu aveva trentadue anni quando generò Serug;
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 Reu, dopo aver generato Serug, visse duecentosette anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 Serug aveva trent'anni quando generò Nacor;
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 Serug, dopo aver generato Nacor, visse duecento anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 Nacor aveva ventinove anni quando generò Terach;
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 Nacor, dopo aver generato Terach, visse centodiciannove anni e generò figli e figlie.
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 Terach aveva settant'anni quando generò Abram, Nacor e Aran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 Questa è la posterità di Terach: Terach generò Abram, Nacor e Aran: Aran generò Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 Aran poi morì alla presenza di suo padre Terach nella sua terra natale, in Ur dei Caldei.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 Abram e Nacor si presero delle mogli; la moglie di Abram si chiamava Sarai e la moglie di Nacor Milca, ch'era figlia di Aran, padre di Milca e padre di Isca.
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 Sarai era sterile e non aveva figli.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 Poi Terach prese Abram, suo figlio, e Lot, figlio di Aran, figlio cioè del suo figlio, e Sarai sua nuora, moglie di Abram suo figlio, e uscì con loro da Ur dei Caldei per andare nel paese di Canaan. Arrivarono fino a Carran e vi si stabilirono.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 L'età della vita di Terach fu di duecentocinque anni; Terach morì in Carran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.

< Genesi 11 >