< 2 Samuele 22 >
1 Davide rivolse al Signore le parole di questo canto, quando il Signore lo liberò dalla mano di tutti i suoi nemici, specialmente dalla mano di Saul.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 «Il Signore è la mia roccia, la mia fortezza, il mio liberatore, Egli disse:
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 il mio Dio, la mia rupe in cui mi rifugio, il mio scudo, la mia salvezza, il mio riparo! Sei la mia roccaforte che mi salva: tu mi salvi dalla violenza.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 Invoco il Signore, degno di ogni lode, e sono liberato dai miei nemici.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Mi circondavano i flutti della morte, mi atterrivano torrenti esiziali.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Mi avviluppavano le funi degli inferi; mi stavano davanti i lacci della morte. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 Nell'angoscia ho invocato il Signore, ho gridato al mio Dio, Egli ha ascoltato dal suo tempio la mia voce; il mio grido è giunto ai suoi orecchi.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Si scosse la terra e sobbalzò; tremarono le fondamenta del cielo; si scossero, perché egli si era irritato.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Fumo salì dalle sue narici; dalla sua bocca uscì un fuoco divoratore; carboni accesi partirono da lui.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 Egli piegò i cieli e discese; una nube oscura era sotto i suoi piedi.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 Cavalcò un cherubino e volò; si librò sulle ali del vento.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 Si avvolse di tenebra tutto intorno; acque scure e dense nubi erano la sua tenda.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 Per lo splendore che lo precedeva arsero carboni infuocati.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 Il Signore tuonò nei cieli, l'Altissimo emise la sua voce.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 Scagliò frecce e li disperse; vibrò folgori e li mise in fuga.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Apparvero le profondità marine; si scoprirono le basi del mondo, come effetto della tua minaccia, Signore, del soffio violento della tua ira.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 Dall'alto stese la mano e mi prese; mi fece uscire dalle grandi acque.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Mi liberò dai miei robusti avversari, dai miei nemici più forti di me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 Mi affrontarono nel giorno della mia rovina, ma il Signore fu il mio sostegno.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 Egli mi trasse al largo; mi liberò, perché oggetto della sua benevolenza.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 Il Signore mi ricompensò secondo la mia giustizia, mi trattò secondo la purità delle mie mani.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Perché mi sono mantenuto nelle vie del Signore, non sono stato empio, lontano dal mio Dio,
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 perché tutti i suoi decreti mi sono dinanzi e non ho allontanato da me le sue leggi.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 Sono stato irreprensibile nei suoi riguardi; mi sono guardato dall'iniquità.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Il Signore mi trattò secondo la mia giustizia, secondo la purità delle mie mani alla sua presenza.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Con il pio ti mostri pio, con il prode ti mostri integro;
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 con il puro ti mostri puro, con il tortuoso ti mostri astuto.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 Tu salvi la gente umile, mentre abbassi gli occhi dei superbi.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 Sì, tu sei la mia lucerna, Signore; il Signore illumina la mia tenebra.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 Sì, con te io posso affrontare una schiera, con il mio Dio posso slanciarmi sulle mura.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 La via di Dio è perfetta; la parola del Signore è integra; egli è scudo per quanti si rifugiano in lui.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 C'è forse un dio come il Signore; una rupe fuori del nostro Dio?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Dio mi cinge di forza, rende sicura la mia via.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Ha reso simili i miei piedi a quelli delle cerve; mi ha fatto stare sulle alture.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Ha addestrato la mia mano alla guerra; ha posto un arco di bronzo nelle mie braccia.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Mi hai dato lo scudo della tua salvezza, la tua sollecitudine mi fa crescere.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Fai largo davanti ai miei passi; le mie gambe non vacillano.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 Inseguo e raggiungo i miei nemici, non desisto finché non siano distrutti.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 Li colpisco ed essi non possono resistere; cadono sotto i miei piedi.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Mi cingi di forza per la battaglia; hai fatto piegare sotto di me i miei avversari.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Mi mostri i nemici di spalle, così io distruggo quelli che mi odiano.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 Gridano, ma nessuno li salva, verso il Signore, che a loro non risponde.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Li disperdo come polvere della terra, li calpesto come fango delle piazze.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Tu mi liberi dalle contese del popolo; mi poni a capo di nazioni; un popolo non conosciuto mi serve.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 I figli degli stranieri mi onorano appena sentono, mi obbediscono.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 I figli degli stranieri vengono meno, lasciano con spavento i loro nascondigli.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 Viva il Signore! Sia benedetta la mia rupe! Sia esaltato il Dio della mia salvezza!
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 Dio fa vendetta per me e mi sottomette i popoli.
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 Tu mi liberi dai miei nemici, mi innalzi sopra i miei avversari, mi liberi dall'uomo violento.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Perciò ti loderò, Signore, fra i popoli canterò inni al tuo nome.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Egli concede una grande vittoria al suo re, la grazia al suo consacrato, a Davide e ai suoi discendenti per sempre».
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”