< Tito 1 >

1 Paulo mitumi wang'wa Itunda hangi mutung'wa wang'wa Yesu Kilisto, kuuhueli wasagulwa ang'wi Tunda nuuhugu wa tai nuileta utaua.
Bulus, bawan Allah, kuma manzon Yesu Almasihu, ta wurin bangaskiyar zababbun mutanen Allah da sanin gaskiya da ta yadda da allahntaka.
2 Akole muuhuili wa upanga wa kale nakale sunga Itunda nisingawiligitya uteele aulagile kuupuma ikale. (aiōnios g166)
Wadannan na cikin begen rai marar matuka wanda Allah, wanda babu karya a cikinsa, ya alkawarta kafin dukkan lokatan zamanai. (aiōnios g166)
3 Kumatungo yayo aulupimilye ulukani lakwe mu mbugulu aumpee une kutanatya. Aizepee kitumo ite kwilago lag'wi Itunda muguni witu.
A daidai lokaci, ya bayyana maganarsa ta wurin sakonsa da ya damka mani in shelar. Zan yi wannan ta wurin umarnin Allah mai ceton mu.
4 Kung'wa Tito ng'wana watai muuhueli witu. Ukende nuuasilya, nuupolo kuupuma kung'wi Tunda tata nuukung'wa Yesu Kilisto muguni witu.
Zuwa ga Titus, da' na gaske a cikin bangaskiyarmu. Alheri, jinkai da salama daga wurin Allah Uba da Almasihu Yesu mai ceton mu.
5 Konsoko eyii ite nikakuleka ku Krete, ingi umazipilye imakani ehi naakele kukonda nukuika ianyampala, akanisa kwa kila kisale anga nainukulagiye.
Sabili da wannan ne na bar ka a Karita domin ka daidaita abubuwan da basu cika ba, ka kuma nada dattibai a dukan birane kamar yadda na umarceka.
6 Munyampala nuuitekelo walekekutula wimelwa, mugoha wa musungu ung'wi, nukete eana ahueli neshanga itegwa kumakani nimabe hangi alekekutula agila anga adabu.
Dole ne dattijo ya zama marar abin zargi, mijin mace daya, da amintattun 'ya'ya wadanda babu wani zargi na mugunta ko rashin kamun kai a kansu.
7 Ingi muhimu kumugozeeli, mu nyumba ang'wi Tunda, alekekutula nikimilwi. Azesinga muntu wiogo ang'wi singawigiilya. Singa wikaya kutaka walekekutula mugala ntule, aleke kutula muntu nuweta wilea, aleketula nsula.
Wajibi ne shugaban Ikklisiya, a matsayin sa na mai kulla da haikalin Allah, ya zama marar aibi. Kada ya zama mai surutu ko rashin hakuri. Kada ya zama mai saurin fushi, ko mashayi, ko mai hayaniya, ko mai handama.
8 Apagwainge: watule muntu musingeeli, mulowa numuzalazima atule muntu nuketi imahala nakondanei, nukete itai muuhueli wang'wi Tunda, nuuimila ung'wenso.
Maimakon haka, ya zama mai karbar baki, abokin abinda ke mai kyau. Dole ne ya zama mai hankali, adali, cike da allahntaka, da kuma kamun kai.
9 Nuhumile kemiila umanyisigwatai namanyisigwe, wahume kuapa nsula na munkolo kumanyisigwe, wahume kuapa nsula na munkolo kumanyisigwa nuuza, hange wakume kuanonelya ehi niakumugilya.
Ya zama mai rike amintaccen sakon da aka koyar da karfi, yadda zai iya karfafa wasu da koyarwa mai kyau ya kuma yi wa wadanda suke hamayya da shi gyara.
10 Kunsoko akule endu asukile nyuma, hangi awo niabadisigwe. Hangi nkani yaupungu. Niaputalya nakuatongela aintu muulimili.
Domin akwai kangararrun mutane dayawa, musamman masu kaciya. Maganganunsu na banza ne. Suna yaudara kuma suna badda mutane.
11 Inonee kuagilya iantu anga nianso. Akumanyisa ayo nishanonee kunsailo aminyala, nukubipya eantu ao ehi.
Wajibi ne mu hana su. Suna koyar da abinda bai kamata su koyar ba saboda makunyaciyar riba suna kuma rusar da iyalai dungum.
12 Ung'wi ao muntu nukete mahala, wikalunga, Wakrete akote uteele nuugila mpelo, abi hangi ikale niitaki, akatahangi alaku.
Daya daga cikinsu, kuma mai hikima ne daga cikinsu, yace, “Kirawa manyan makaryata ne, lalatattu kuma miyagun dabbobi, masu kyiuya da zarin cin abinci.”
13 Ingi inkazi yatai, ite gwa uagilye kungulu, ahume kutambula itai muhuueli.
Wannan magana gaskiya ne, ka yi masu gyara da tsanani yadda zasu kafu a cikin bangaskiya.
14 Uewe ulekekihangwila mumahumo nisingaatai, akiyahudi ang'wi malago aantu, niisusha ikenyuma itai.
Kada ka mai da hankalin ka ga tatsunniyoyi na Yahudawa ko dokokin mutane wadanda sun sauya gaskiya.
15 Kuawa ehi niaza, maintu ehi ni maza. Kuawa ehi niabe nawaga niagila uuhueli kutile nikiza. Kunsoko imasego ao nusinganilye wao wabipile.
Ga wadanda suke da tsarki, komai mai tsarki ne. Amma wadanda suke marasa tsarki da rashin bangaskiya, komai marar tsarki ne. Domin zuciyarsu da lamirinsu sun gurbata.
16 Akulunga amumanyile Itunda, lakini kuntendo yao amuhitile. Nianso anyamilandu nishanga agombile. Nishangaahoiwe kuluka ni lehi nuluza.
Suna cewa sun san Allah, amma sun musanta shi ta wurin ayyukansu. Sun zama abin kyama da marasa biyayya. Ba za a iya tabbaatar dasu ba akan wani aiki maikyau.

< Tito 1 >