< Luka 5 >
1 Aitulikile matungo iantu akizura nakumupilimilya U-Yesu nukumutegelya ulukani Langwi Itunda, nai wimikile panipelo aluzi la Genesareti.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Auine mabine abili Imikingwe kupelo aluzi Iaibua Samaki aiapumaa aiakoja inyabu yao.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 U-Yesu akingila mibini, nai lang'wa Simoni na akalompa atwale ibini muluzi kuli inino nihi ninyumu. hangi akikie kumumanyisa kupuma mibini.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Akaligitia, akamuila U-Simoni litwale ibini lako muluzi uisimie inyabu yako utule bua Insamaki.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Simoni akasusha nukulunga, tata kituma, aimilimo uliku wihi, Shakupatile anga kintu kihi hangi kulukani lako kuisimya inyabu.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Naitumile uu ikahoela Insamaki iduu na lyabu yao yika tula tinike.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Ikaitanga Iabuani ao kibini Ingiza hangi aze kua ailya. Ikaza akizulia imabini ihi ikatula kilieka mukati muluzi.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Hangi Simoni Petro nauine uu, akatugama na malu pang'wa Yesu akalunga;''Hega kitalane, kunsoko une ni muntu wamilandu tata.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Kunsoko akapata ikuilwa ihi naine kunsamaki naiatendile.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Ulu iti aliakuile uYakobo na Yohana ng'wana wang'wa Zebedayo aipulug'wi nu Simoni. Nu Yesu akamuila uSimoni kandya itungili apana kogopa kumbele ukutula bua iantu.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Naiamaletile imabini ao mihi ni nyumu, kaleka kintu kihi ikamutyata nuanso.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Niipumie naukali mukisali muntu naukete ibili kuko, matungo namuine U-Yesu augwie akakumana pihi nukulompa, akalunga,''tata ang'wi uloiwe umponie.''
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Sunga U-Yesu akahumbula umukona nukumuamba, akalunga ndoilwa ukomie itungo lilo imbili iakahega.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Akamuile alekekumuila anga muntu wihi, akamula longala wionyeshe nu utemi upumie isongiliyo.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Kulula ikani yakwe ikasambaila kui, numilundo wa antu ukaza palung'wi nukumutigelya numanyisa nukuguna imalwae ao.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Ingi hapu hapuu akikie wingene akazilompa.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Aituile luhiku lungwi nema hiku ayo naukumanyisa, aiokoli Mafarisayo niamanyisa anonya nkai akikie hapo aizile kupuma muisali ningiza numukisali kang, wa Galilaya nanu Yudea, hangi nukupuma mukisali kang'wa Yerusalemu. Ingulu yang'wa tata akali palung'wi nung'wenso kuguna.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 antu akehu aiazile, ainkenkile mundili umuntu nuigandi naikai ikaduma inzila akumingilya mukati amulalishe pihi kuntongela ang'wa Yesu.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Shaikapata inzila akumingilya mukati kunsoko umilundo, ukanankila migulya milialo lanyumba ikamusunta muntu nuanso pihi kukiila mibolomya migulya mundili akwe mukati wa antu kuntongela lukulu pang'wa Yesu.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Akazigoza uhuili wakwe, Yesu akalunga muhumba miane, imilandu ako wasamehelwa.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Anumwa nkani ni mafalisayo ikandya kukolya nulanso, akalunga uyu nyenyu nukuligitya kuubii? Nyenyu nuhumile kusamehela imilandu ingi Itunda du nuing'wine?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Ingi u Yesu ainualinga ntuni naiakukisiga, akasukilya, nukuaila, kuniki nimukikolya mukolo yanyu?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Nikiuli nikipepele kulugilya, Imilandu ako alekwa ang'wi kulunga uka ugende?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Ingi mulinge gwa ung'wana wang'wa Adamu ukite uhumu muukumbigulu kusamehela imilandu, kuila uewe uka uhole indili ako ulongole kitalako.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Imatungo yayo yayo akauko meleao nukuhola indili akwe naulaie. Hangi akasuka kitalakwe nukumukulya Itunda.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Ingi kila ung'wi ao akakuilwa nukumukulya Itunda. Ikizuilwa nuao, ikalunga, kuine ikani shanga nzaile liyi.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Ingi inkani nianso kupumila, u Yesu akahega kung'wanso akamuona umuhoela mpia naiwitang'wa Lawi wikie mukisali kakuhoela mpia. Akamuiila, ntwate.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Ingi u Lawi akahumbuka nukumuntwata, akaleka kila kintu kunyuma.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Ingi u Lawi akanunelya munyumbakwe isikukuu ninkulu kunsoko ang'wa Yesu. Aiakoli iahoela mpia indu kung'wanso ni antu indu naiikie pameza akizilya palung'wi nienso.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Hangi mafalisayo aiakuanung'u nikila iamanyisigwa akizilunga, kuniki nimukulya nukung'wa niahoela mpia palung'wi ni antu niangiza niakite milandu?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 U Yesu akasusha, iantu niakite upanga nuuza shaatakile itabibu, ingi ao nialwaeli niaamutakile ung'wi.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Shainzile kuitanga iantu makite itai ahume kugunwa, ingi ainziitanga nia milandu ahume kugunwa.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Ikamuila, iamanyisigwa ang'wa Yohana a hapouifunga nukulompa, ni amanyisigwa ang'wa mafalisayonienso itenda uu, Ai amanyisigwa ako iliza nukung'wa.
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 U Yesu akaaila, ihumile muntu wihi kituma naiendile muwinga kumunyawinga, matungo numunyawinga, kilukoli palung'wi nienso?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Ingi imahiku aziziza imatungo umunyamwinga nuzi hegigwa kitalao, lulo luhiku lakufunga.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Ingi u Yesu akaligitya kitalao kwakilingasilyo. Hutile nukutamula inino ung'wenda kupuma mivazi nipya nukutumila kunonelya ivazi nilakali. Anga watende uu, ukutamula ung'wenda.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Hangi kutile anga muntu nuika idivai nimpya muuriba nunkulukulu, inga angitume uu, idivai nimpya aizitamula. Ikiseme ni divai aizihunuka iriba aiyizigazika.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Ingi idivai nimpya iikwe muiliba nimpya.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Kutile umuntu hangi nukung'wa idivai na kali, shukulowa nimpya kunsoko ukulunga na kali nza.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”