< Luka 14 >

1 Aeipumie luhiku lakumukulya, naulongoe munyumba ang'wi ao nuatongeli a Mafarisayo kulya mukate, neenso akumugoza kwa pakupe.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 Goza, pantongelakwe aukole muntu nuanso aukagigwa nuuimbwa.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 U Yesu wakaakolya eamanyi kupuma milago la Ayahudi ne Mafarisayo, “Ite izane kumukomya umuntu uluhiku lakukulya, anga singauu?”
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 Lakini nianso akilagilye ihetwe, kuite u Yesu wakamuamba, wekamukomya wikamulekela alongole yakwe.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 Nung'wenso wikamuila, “Nyenyi apaite nukite ung'wana ang'wi ng'ombe wagwila muluze luhiku la kukulya shanga ukumuluta kunzi wapume?”
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 Nianso aeagila anga uhumi wakupumya ulukani kunkani niyanso.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 Imatungo u Yesu nauagundue naile naalekilwe kina asagae intu niyaheshima, akaaila, kupyani akaaila.
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 Imatungo nimalekilwe numuntu kuwinga, ukekikie munafasi naheshima, kunsoko iwezekanile walikilwe muntu mungiza nukite heshima kukila uewe.
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 Imatungo umuntu nualekilwe unye nimeabiile angawapike, ukuela uewe, “muhegele uyu enafasi ako” kuite kwa minyala ukonza kuhega nukikie kunyuma.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Lakini uewe angawalekwe, longola wikie kumwisho ite imatungo angawaza nukualekile, uhumile kuuila uewe, muhumba miane, longola kuntongela kukila.” Kuite ukutula uheshimiwe ntongela aehi neikie palung'wi nuewe pameza.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 Kundogoilyo uyu nuikulya wisimigwa, nuyu nuisimya wikuligwa.
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 U Yesu akamuila umuntu naumalekile, “Nukupumya indya ya mung'wi ang'wi yampende, lakukualeka eahumba eako ang'wi anya ndugo ako ang'wi antu ang'wi anyakisale ako neatajili, ite kunsoko neaenso akekualika uewe upate ilipo.
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 Kuleka ite, nukuanya isherehe, aaleke eamasikini, ealema, akewete, niapoku,
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 nuewe ukukembetwa, kunsoko shangaakulipa. Kundogoelyo ukulipwa muwioki watai.”
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 Imatungo ung'wi ao aewikie mumeza palung'wi nu Yesu naewigule aya, nung'wenso wikaaela, “Ukembetilwe nuanso nuekulya umukute muutemi wang'wi Tunda.
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 Lakini u Yesu wikaaila, “Muntu ung'we auzepilye sherehe nkulu, akaitanga antu eedu.”
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 Matungo isherehe naekole tayari, aumutumike umitumi akwe aaele awa naalekilwe, “Pembyi mihi kunsoko iintu yehi ikole tayali.
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 Ehi, ekatulalompa radhi. Nuang'wandyo akamuila umitumi, ngoile mugunda, lazima nende nulegoze. Itunu unsamile.
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 Numuya wikalunga, Nguile majoki ataano na ng'ombe, nunene niinzu kuagema, itunu unkoelwe.
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 Nu muntu mungiza wekalunga, “Ntenile musungu, kuite shanga nzile.”
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 Umitumi akasuka akamuila umukulu wakwe emakani nanso. Umukola nyumba wikataka akamuila umitumi wakwe, “Longokaya muisale numukona akisale ualete hapa iamasikini, niakelema, niapoku nawa nialemilwe.”
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 Umitumi wikalunga, mkulu aya nazundagiye ehi namituma, ganitungile ga enafasi kele ekole.”
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 Mukulu wikamuila umitumi, longola munzila nenkulu uahimize eantu ingiile, ite enyumba ne izule.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 Kundogoelyo kumuila, kuite awa nialekilwe nung'wandyo shangaukuonza esherehe ane.
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Ite umati ukulu aealongoe palung'wi nung'wenso, nung'wenso wikapiluka, wikaaila,
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 Angize muntu wizile kitalane nung'wenso shangaumubipiwe utata akwe, musungu wakwe, anaaakwe, anyandugu akwe, agoha nawa niasungu ee, ga nuwikale wakwe ga shanga ukutula mumanyisigwa wane.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 Umuntu nushanga ukuhola umusalaba wakwe waze kunyuma ane shanga uhumile kutula mumanyisigwa wane.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 Kundogoelyo nyenyu ung'wi anyu, nuhumilwe insula akuzenga umunola shanga ukikie hanza wakadilie engalama kumahesabu kina ukite eke nutakile wahu kukamisha nelanso?
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 Kuite, baada akuika umusingi nukuleng'wa kumala, ehi naineakanza kumugema.
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 Akutambula umuntu uyu aewandilye kuzenga, wekatula mugila anga ngulu akumailya.”
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 Ite mutemike, nutakile kenda kikua nuutemi nuungiza kumbita, shanga uhumile kikie hanza pihe nukuhola imasigo angize uhumile, palung'wi ni antu elfu ikumi kikua nuutemi nuungiza nuukiza migulya akwe neantu elfu ishilini?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 Kang'wi shangauu, matungo ijeshi nilaangiza kile lekole kule, wetuma momboi kutaka emashariti aamani.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 Kuite gwa, wehi ung'wi ao neshanga ukuleka ehi nanso nukete, shanga uhumile kutula mumanyisigwa ane.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 Umunyu uza, lakini anga umunyu angaulimilye lauha akwe, ikutula ule utule munyu hange?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 Ngila anga matumizi muudogo hata mumbolea uyu nakite iakutwe ahija nuije.”
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Luka 14 >