< Mazmur 83 >

1 Mazmur Asaf: suatu nyanyian. Ya Allah, janganlah Engkau bungkam, janganlah berdiam diri dan janganlah berpangku tangan, ya Allah!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Sebab sesungguhnya musuh-musuh-Mu ribut, orang-orang yang membenci Engkau meninggikan kepala.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Mereka mengadakan permufakatan licik melawan umat-Mu, dan mereka berunding untuk melawan orang-orang yang Kaulindungi.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Kata mereka: "Marilah kita lenyapkan mereka sebagai bangsa, sehingga nama Israel tidak diingat lagi!"
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Sungguh, mereka telah berunding dengan satu hati, mereka telah mengadakan perjanjian melawan Engkau:
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Penghuni kemah-kemah Edom dan orang Ismael, Moab dan orang Hagar,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal dan Amon dan Amalek, Filistea beserta penduduk Tirus,
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 juga Asyur telah bergabung dengan mereka, menjadi kaki tangan bani Lot. (Sela)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Perlakukanlah mereka seperti Midian, seperti Sisera, seperti Yabin dekat sungai Kison,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 yang sudah dipunahkan di En-Dor, menjadi pupuk bagi tanah.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Buatlah para pemuka mereka seperti Oreb dan Zeeb, seperti Zebah dan Salmuna semua pemimpin mereka,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 yang berkata: "Marilah kita menduduki tempat-tempat kediaman Allah!"
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Ya Allahku, buatlah mereka seperti dedak yang beterbangan, seperti jerami yang ditiup angin!
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Seperti api yang membakar hutan, dan seperti nyala api yang menghanguskan gunung-gunung,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 kejarlah mereka dengan badai-Mu, dan kejutkanlah mereka dengan puting beliung-Mu;
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 penuhilah muka mereka dengan kehinaan, supaya mereka mencari nama-Mu, ya TUHAN!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Biarlah mereka mendapat malu dan terkejut selama-lamanya; biarlah mereka tersipu-sipu dan binasa,
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 supaya mereka tahu bahwa Engkau sajalah yang bernama TUHAN, Yang Mahatinggi atas seluruh bumi.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Mazmur 83 >