< Genesis 32 >

1 Intuloy met ni Jacob ti panagdaliasatna, ket sinabat isuna dagiti anghel ti Dios.
Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
2 Idi nakita ida ni Jacob, kinunana, “Daytoy ket kampo ti Dios”, isu nga inawaganna dayta a lugar iti Mahanaim.
Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
3 Nangibaon ni Jacob kadagiti mensahero nga umun-una ngem isuna a mapan iti kabsatna a ni Esau, iti daga ti Seir, iti rehion ti Edom.
Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
4 Binilinna ida, a kunana, “Kastoy ti ibagayo iti apok a ni Esau: Kastoy ti kuna ti adipenmo a ni Jacob: 'Nakipagnanaedak kenni Laban, ket nagtalinaedak a nakipagnanaed aginggana ita.
Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
5 Addaanak kadagiti baka, asno, ken arban, lallaki nga adipen, ken babbai nga adipen. Nangibaonak tapno maibaga daytoy iti apok, tapno makasarakak koma iti pabor iti imatangmo.”'
Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
6 Nagsubli dagiti mensahero kenni Jacob ket kinunada, “Napankami iti kabsatmo a ni Esau. Umaynaka sabten, ket adda kaduana nga uppat a gasut a lallaki.
Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
7 Ket nagbuteng ken nariribukan ni Jacob ti kasta unay. Isu a biningayna dagiti tattao a kaduana iti dua a kampo, ken kasta met dagiti arban ti karnero ken kalding, baka, ken dagiti kamelyo.
Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
8 Kinunana, “No umay ni Esau iti maysa kadagiti kampo ket darupenna daytoy, aglibasto ti maysa a kampo.”
Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
9 Kinuna ni Jacob, “Dios ti amak a ni Abraham, ken Dios ti amak a ni Isaac, Yahweh, a nagkuna kaniak, 'Agsublika iti pagiliam ken kadagiti kakabagiam, ket parang-ayenkanto,'
Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
10 Saanak a maikari iti amin nga aramidmo a nangipakita iti kinapudnom iti katulagan ken iti amin a kinamatalek nga inaramidmo para iti adipenmo. Ta sarukod laeng ti awitko idi bimmallasiwak iti daytoy a Jordan, ket ita nagbalinakon a dua a kampo.
Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
11 Pangnga-asim ta ispalennak manipud iti ima ti kabsatko, manipud iti ima ni Esau, ta mabutengak kenkuana, nga umay isuna ket darupennak ken dagiti inna a kadua dagiti ubbing.
Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
12 Ngem kinunam, 'Pudno a parang-ayenkanto. Pagbalinekto dagiti kaputotam a kasla darat iti baybay, a saan a mabilang iti kinaaduda.”'
Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
13 Nagtalinaed ni Jacob sadiay iti dayta a rabii. Nangala isuna iti sumagmamano kadagiti adda kenkuana a kas sagut a maipaay kenni Esau, a kabsatna:
Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
14 dua gasut a kabaian a kalding ken duapulo a kalakian a kalding, dua gasut a kabaian a karnero ken duapulo a kalakian a karnero,
awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
15 tallopulo nga agpagpagatas a kamelio ken dagiti urbonda, uppat a pulo a kabaian a baka ken sangapulo a kalakian a baka, duapulo a kabaian nga asno ken sangapulo a kalakian nga asno.
raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
16 Impaaywanna dagitoy kadagiti adipenna, maysa nga arban iti tunggal adipen. Kinunana kadagiti adipenna, “Umunakayo kaniak ket ikkanyo iti pagbaetan ti tunggal arban.”
Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
17 Binilinna ti umuna nga adipen, a kunana, “Inton masabatnaka ni Esau a kabsatko ken agsaludsod kenka, a kunana, 'Siasino ti nakaibilangam? Sadino ti papanam? Ken siasino ti makinkukua kadagitoy nga ayup iti sangoanam?'
Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
18 Ket ibagamto a, 'Dagitoy ket kukua ti adipenmo a ni Jacob. Dagitoy ket sagut a naipatulod para iti apok a ni Esau. Ket makitamto, sumarsaruno isuna kadakami,'”
Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
19 Binilin ni Jacob ti maikadua a bunggoy, ti maikatlo, ken dagiti amin a tattao a mangsarsaruno kadagiti arban. Kinunana, “Ibagayo ti isu met laeng a banag kenni Esau inton makitayo isuna.
Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
20 Ibagayo met a, “Sumarsaruno kadakami ti adipenmo a ni Jacob.'” Ta pinanunotna nga, “Ay-ayoek isuna babaen kadagiti sagut nga ummun-una kaniak. Inton makitak isuna, barbareng no awatennakto.”
Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
21 Isu nga immuna a napan dagiti sagut ngem isuna. Nagtalinaed isuna iti dayta a rabii iti kampo.
Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
22 Bimmangon ni Jacob iti dayta a rabii, ket inkuyogna dagiti dua nga assawana, dagiti dua a babai nga adipenna, ken dagiti sangapulo ket maysa a putotna a lallaki. Imbaonna ida iti ballasiw ti waig ti Jabbok.
A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
23 Iti kastoy a wagas, imbaonna ida iti ballasiw ti waig kasta met dagiti amin a sanikuana.
Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
24 Nabati nga agmaymaysa ni Jacob, ket maysa a lalaki ti nakigabbo kenkuana inggana iti panagsingising ti init.
Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
25 Idi nakita ti lalaki a saanna a maabak isuna, dinapigna ti patong ni Jacob. Naglagisi ti patong ni Jacob kabayatan a makigabgabbo isuna kenkuana.
Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
26 Kinuna ti lalaki, “Palubosannakon, ta sumingsingisingen ti init.” Kinuna ni Jacob, “Saanka a palubosan malaksid no bendisionannak.”
Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
27 Kinuna ti lalaki kenkuana, “Ania iti naganmo? Simmungbat ni Jacob, “Jacob.”
Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
28 Kinuna ti lalaki, “Ti naganmo ket saanen a Jacob, no di ket Israel. Ta nakibinnalubalka iti Dios ken kadagiti tattao ket nangabakka.”
Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
29 Sinaludsod ni Jacob kenkuana, “Pangngaasim ta ibagam kaniak ti naganmo.” Kinunana, “Apay a salsaludsudem ti naganko?” Ket binendisionanna isuna sadiay.
Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
30 Pinanaganan ni Jacob ti lugar a Peniel ta kinunana, “Nakitak ti Dios iti rupan-rupa, ket naisalakan ti biagko.”
Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
31 Lumgaken ti init idi pumanaw ni Jacob idiay Peniel. Agpilaypilay isuna gapu iti patongna.
Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
32 Dayta ti makagapu no apay nga agingga iti daytoy nga aldaw ket saan a kankanen dagiti tattao ti Israel ti pennet iti patong nga adda iti nagsuopan iti patong, gapu ta dinangran ti lalaki dagidiay a pennet bayat iti panaglagisi ti patong ni Jacob.
Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.

< Genesis 32 >