< Dagiti Aramid 1 >
1 Ti immuna a libro nga insuratko, O Teofilo, imbagana amin dagiti inrugi ni Jesus nga aramiden ken isuro,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 agingga iti aldaw a naawat isuna sadiay ngato. Daytoy ket kalpasan nga intedna ti bilin babaen iti Espiritu Santo kadagiti pinilina nga apostol, nga isu dagiti nagparanganna a sibibiag
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 kalpasan iti panagsagsagabana. Iti uppat a pulo nga al-aldaw, intultuloyna ti nagparang kadakuada, nangibagbaga kadagiti banbanag a maipanggep iti pagarian ti Dios.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 Idi nakisinnarak isuna kadakuada, imbilinna a saanda a panawan ti Jerusalem, ngem urayenda ti kari iti Ama, a kinunana, “Nangngegyo manipud kaniak
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 a pudno unay a nangbautisar ni Juan babaen iti danum, ngem mabautisarankayto babaen iti Espiritu Santo, iti mabiit.”
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 Idi naummongda, sinaludsodda kenkuana, “Apo, daytoy kadin ti tiempo nga isublim ti pagarian iti Israel?”
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 Kinunana kadakuada, “Saan a para kadakayo ti mangammo iti tiempo wenno iti panawen nga inkeddeng ti Ama babaen iti bukodna a turay.
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 Ngem umawatkayonto iti pannakabalin, inton umay kadakayo ti Espiritu Santo, ket dakayonto dagiti saksik idiay Jerusalem ken iti amin a Judea ken Samaria, ken kadagiti sulsuli ti daga.”
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 Idi naibagan ni Apo Jesus dagitoy a banbanag, bayat a kumitkitada sadiay ngato, naipangato isuna, ket inlemmeng isuna iti ulep manipud kadagiti matada.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 Kabayatan iti napinget a panangkitada iti langit bayat a mapmapan isuna, kellaat nga adda dua a lallaki a nakapuraw a nakatakder ti abayda.
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 Kinunada, “Dakayo a lallaki iti Galilea, apay a nakatakder kayo ditoy a kumitkita idiay langit? Daytoy Jesus a nagpangato idiay langit ket agsublinto iti wagas a kas metlaeng iti nakitayo a pannakaipangatona sadi langit.”
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Kalpasanna, nagsublida idiay Jerusalem manipud idiay Bantay ti Olibo, nga asideg iti Jerusalem, a madalliasat iti kas kapaut ti Aldaw a Panaginana.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 Idi nakasangpetdan, napanda iti akin-ngato a siled, nga isu iti pagigiananda. Isuda da Pedro, Juan, Santiago, Andres, Felipe, Tomas, Bartolome, Mateo, Santiago nga anak ni Alfeo, Simon a Patriota, ken Judas nga anak ni Santiago.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 Sangsangkamaysada amin a sipapasnek a nangitultuloy iti panagkararag. Ket karaman ditoy dagiti babbai, ni Maria nga ina ni Jesus, ken dagiti kakabsat ni Jesus a lallaki.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 Kadagidiay nga al-aldaw, timmakder ni Pedro iti nagtetengngaan dagiti kakabsat, agarup sangagasut ket duapulo a tattao, ket kinunana,
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 “Kakabsat, nasisita a matungpal ti Nasantoan a Surat, nga insaksakbay nga insao ti Espiritu Santo babaen iti ngiwat ni David maipapan kenni Judas, nga isu iti nangidaulo kadagiti nangtiliw kenni Jesus.
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 Ta maysa met isuna kadatayo ken inawatna ti bingayna kadagiti pagnumaran iti daytoy a ministerio.”
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 (Tatta, daytoy a lalaki ket nakagatang iti taltalon babaen iti birok ti dakes nga aramidna. Kalpasanna, natinnag nga umuna ti ulona, ken bimtak ti bagina, ket amin a lalaem iti tianna ket naiburais.
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 Naammoan daytoy dagiti amin nga agnanaed idiay Jerusalem, isu nga iti bukodda a pagsasao, inawaganda dayta a taltalon iti “Akeldama,” dayta ket, “Kataltalunan ti Dara.”)
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 Ta naisurat iti Libro dagiti Salmo, 'Mabaybay-an koma dagiti taltalonna, ken awan koma ti uray a tao nga agnaed sadiay'; ken, 'Maipasublat koma iti sabali ti takemna a kinamangidadaulo.'
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 Nasisita ngarud, a maysa kadagiti lallaki a kimmuykuyog kadatayo iti amin a tiempo a kaadda ni Apo Jesus kadatayo,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 manipud idi nangrugi a nangbautisar ni Juan agingga iti aldaw a naala ni Jesus manipud kadatayo, masapul a kaduatayo a saksi iti panagungarna.”
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 Impasangoda dagiti dua a lallaki, ni Jose a maawagan Barsabas, a managan met laeng iti Justo, ken ni Matias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 Nagkararagda ket kinunada, “Sika, Apo, ammom ti adda iti puspuso iti amin a tattao, isu nga ipaltiingmo koma no siasino kadagitoy a dua ti napilim
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 a mangsublat iti akem iti daytoy a ministerio ken kinaapostol a linabsing ni Judas iti ipapanna iti bukodna a lugar.”
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 Binunotda no siasino kadakuada ti napili ket nabunot ni Matias. Ket naibilang isuna kadagiti sangapulo ket maysa nga apostol.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.