< 2 Mózes 22 >

1 Ha valaki ökröt vagy bárányt lop, és levágja vagy eladja azt: öt barmot fizessen egy ökörért, és négy juhot egy bárányért.
“In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
2 Ha ház-fölverésen kapják a tolvajt, és úgy megverik, hogy meghal, nincs vérbűn miatta.
“In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
3 Ha reá sütött a nap, vérbűn van miatta: fizessen; ha nincs néki: adassék el tolvajságáért.
amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
4 Ha elevenen kapják kezében a lopott jószágot, akár ökör, akár szamár, akár juh: két annyit fizessen érette.
In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
5 Ha valaki mezőt vagy szőlőt étet le, úgy hogy barmát elereszti, és az a más mezején legel: mezejének javából és szőlőjének javából fizesse meg a kárt.
“In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
6 Ha tűz támad, és tövisbe kap, és megég az asztag, vagy a lábon álló gabona, vagy a mező: fizesse meg a kárt, a ki a tüzet gyujtotta.
“In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
7 Ha valaki pénzt vagy edényeket ád felebarátjának megőrzés végett, és ellopják annak a férfiúnak házából: ha megtalálják a tolvajt, fizessen kétannyit.
“In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
8 Ha nem találják meg a tolvajt, a ház urát vigyék a bírák eleibe: hogy nem nyújtotta-é ki kezét az ő felebarátja vagyonára.
Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
9 Akármi bűn dolgában, akár ökör, akár szamár, akár juh, akár ruha, akármi elveszett jószág az, a miről azt mondja: ez az; mindkettőjük ügye a bírák eleibe menjen, és a kit a bírák bűnösnek mondanak, fizessen két annyit az ő felebarátjának.
A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
10 Ha valaki szamarat, vagy ökröt, vagy bárányt, vagy akármiféle barmot ád az ő felebarátja gondviselése alá, és az elhull, vagy megsérül, vagy elhajtatik, úgy hogy senki sem látta:
“In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
11 Az Úrra való esküvés legyen kettejök közt, hogy nem nyújtotta-é ki kezét felebarátja vagyonára; és ezt fogadja el annak ura, és az semmit se fizessen.
rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
12 Ha pedig ellopták tőle: megfizesse az urának.
Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
13 Ha széttépetett, hozza el azt bizonyságul; a széttépettet nem fizeti meg.
In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
14 Ha pedig valaki kölcsön kér az ő felebarátjától, és az megsérül vagy elhull urának távollétében: fizesse meg a kárt.
“In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
15 Ha ura vele van, nem fizet; ha bérbe adatott, bérébe megy.
Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
16 Ha valaki hajadont csábít el, a ki nincs eljegyezve, és vele hál: jegyajándékkal jegyezze azt el magának feleségül.
“Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
17 Ha annak atyja nem akarja azt néki adni: annyi pénzt adjon, a mennyi a hajadonok jegyajándéka.
In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
18 Varázsló asszonyt ne hagyj életben.
“Kada ku bar maiya da rai.
19 A ki barommal közösül, halállal lakoljon.
“Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
20 A ki isteneknek áldozik, nem csupán az Úrnak, megölettessék.
“Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
21 A jövevényen ne hatalmaskodjál, és ne nyomorgasd azt, mert jövevények voltatok Égyiptom földén.
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22 Egy özvegyet vagy árvát se nyomorítsatok meg.
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23 Ha nyomorgatod azt, és hozzám kiált, meghallgatom az ő kiáltását.
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24 És felgerjed haragom, és megöllek titeket fegyverrel, és a ti feleségeitek özvegyekké lésznek, a ti fiaitok pedig árvákká.
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
25 Ha pénzt adsz kölcsön az én népemnek, a szegénynek a ki veled van; ne légy hozzá olyan, mint a hitelező; ne vessetek reá uzsorát.
“In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
26 Ha zálogba veszed a te felebarátod felső ruháját: naplemente előtt visszaadd azt néki:
In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
27 Mert egyetlen takarója, testének ruhája az: miben háljon? Bizony, ha én hozzám kiált, meghallgatom; mert én irgalmas vagyok.
domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
28 A bírákat ne szidalmazd, és néped fejedelmét ne átkozd.
“Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
29 Gabonáddal és boroddal ne késlekedjél; fiaid elsőszülöttét nékem add.
“Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
30 Hasonlóképen cselekedjél ökröddel, juhoddal; hét napig legyen az ő anyjával, a nyolczadik napon nékem add azt.
Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
31 És szent emberek legyetek én előttem; a mezőn széttépett húst meg ne egyétek; az ebnek vessétek azt.
“Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.

< 2 Mózes 22 >