< Zsoltárok 59 >

1 A karmesternek. Ne ronts szerint. Dávidtól dal. Mikor Sául oda küldött és őrizték a házát, hogy megöljék. Ments meg engem ellenségeimtől, Istenem, támadóimtól ótalmazz engem!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Ments meg a jogtalanságot cselekvőktől, és a vérontás embereitől segíts meg!
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 Mert íme lestek lelkemre, összesereglenek ellenem erősek; se bűntettem, se vétkem nincsen, oh Örökkévaló!
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Bűnöm nélkül sürögnek és készülődnek; serkenj elibém és lásd!
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 És te, oh Örökkévaló, Isten, seregek ura, Izraél Istene, ébredj, megbüntetni mind a nemzeteket, ne kegyelmezz mind a jogtalan hűtelenkedőknek! Széla.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 Estére visszatérnek, mordúlnak, mint az eb, s körüljárják a várost.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Íme, szót bugyogtatnak szájukkal, kardok az ajkaikon, mert ki hallja!
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 Te pedig, Örökkévaló, nevetsz, rajtuk, gúnyolódol mind a nemzeteken.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Erőm! Te rád hadd várok, mert Isten a mentsváram.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 Szeretetem Istene elémbe jön, Isten néznem engedi meglesőimet.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 Ne öld meg őket, nehogy elfelejtse népem, bujdostasd őket hatalmaddal, és döntsd le őket, oh paizsunk, Uram.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 Szájuk vétke, ajkuk szava által fogassanak meg gőgjükben, az esküdözés miatt és hazudozás miatt, melyeket mondogatnak.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Semmísítsd meg hévvel, semmisítsd, hogy ne legyenek; és megtudják, hogy Isten uralkodik Jákóbon a föld végeig. Széla.
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 S visszatérnek estére, mordúlnak mint az eb, s hörüljárják a vá. rost.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 Ők bujdosnak eledel után, ha nem laknak jól, úgy kell meghálniok.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 Én pedig énekelem erődet, és újjongok reggelre szereteteden; mert mentsvárul voltál nekem s menedékem, a mely napon megszorultam.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 Erőm, rólad hadd zengek mert Isten az én mentsváram, szeretetem Istene.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Zsoltárok 59 >