< Jób 37 >

1 Igenis, ezért remeg szívem s felszökken helyéből.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Hallva halljátok hangja háborgását s a morajt, mely szájából kél;
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 az egész ég alatt van terjedése és fénye a föld szélein.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Utána ordít a hang: dörög fenséges hangján, s nem tartja vissza, midőn hallatszik hangja.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Csodásan dörög Isten a hangján, nagyokat tesz, s nem ismerjük meg.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Mert a hónak mondja: szállj a földre, meg a hulló esőnek, hatalmasan hulló esőjének
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Minden ember kezét lepecsételi, hogy megismerje alkotását minden halandó.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 S bemegy a vad a leshelyre, és tanyáiban lakozik.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 A kamarából szélvész jő és a szóró szelektől a hideg.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Isten leheletétől jég keletkezik s a vizek tágassága szilárddá lesz.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Nedvességgel meg is terheli a felleget, szétterjeszti fényének felhőjét.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 S az körökben egyre forog, kormányzása által, cselekvésök szerint, bár mire rendeli őket a földkerekség színén;
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 hol ostorul, ha földjének javára van, hol szeretetre nyújtja.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Figyelj erre, Jób, állj meg és vedd észre Isten csodáit!
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Tudsz-e róla, midőn Isten ügyel rájuk, s tündökölteti felhőjének fényét?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Tudsz-e a fellegnek lengéséről, a tökéletes tudásúnak csodáiról?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Te, kinek melegek a ruhái, midőn a földet pihenteti a déli szél által.
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Vele boltozod a mennyeket, melyek erősek, mint a szilárd tükör?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Tudasd velünk, mit mondjunk neki! Mit sem hozhatunk fel a sötétség miatt.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Jelentetik-e neki, hogy beszélek, avagy szólt-e ember, hogy elpusztíttassék?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Most ugyan nem látni a fényt, mely ragyogó a mennyekben; de a szél átvonul s megtisztítja azokat.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Észak felől arany jön, Isten mellett félelmes fenség.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 A Mindenhatót, nem érjük őt fel, a nagy erejűt, de a jogot és teljes igazságot nem sérti meg.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Azért félik őt az emberek, nem nézi ő mind a bölcsszívűeket.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Jób 37 >