< Jób 12 >
2 Valóban, ti vagytok ám a nép, s veletek kihal a bölcsesség!
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Nekem is van szívem mint nektek, nem esem messze tőletek, hisz kinél nem volnának effélék?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Nevetségéül vagyok barátnak, ki Istent szólította s ő meghallgatta; nevetségül az igaz, a gáncstalan!
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 A balvégzetnek megvetés, a gondtalannak vélekedése szerint, készen áll, a tántorgó lábúaknak.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Boldogságban vannak a rablók sátrai és biztosság azoké, kik Istent haragítják, azé, ki istenét kezében hordja.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Azonban kérdezd csak meg a barmot, majd tanít téged, s az ég madarát, majd megjelenti neked;
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 vagy szólj a földnek, majd tanít téged, és elbeszélik neked a tenger halai.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Ki ne tudná mindezekből, hogy az Örökkévaló keze cselekedte ezt;
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 kinek kezében van minden élőnek a lelke, s minden ember testének a szelleme.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Nemde a fül vizsgálja a szavakat s az íny az ételt ízleli meg?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 Aggastyánokban van bölcsesség, s hosszú élet: értelmesség.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Ő nála van bölcsesség és erő, övé tanács és értelmesség!
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Lám, lerombol s nem építtetik föl, rázár valakire s nem nyittatik ki neki.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Im elrekeszt vizeket s kiszáradnak – megereszti őket s feldúlják a földet.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Ő nála van hatalom és üdvösség, övé a tévelygő és a megtévesztő.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Járatja a tanácsosokat megfosztottan s a bírákat megtébolyítja;
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 a királyok kötelékét föloldotta és reákötött övet az ő derekukra;
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 járatja a papokat megfosztottan s a szilárdakat elferdíti;
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 megvonja a biztosszavúak beszédjét s a véneknek eszét elveszi;
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 csúfot önt a nemesekre s a hatalmasoknak kötését meglazítja.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Feltár mély dolgokat a sötétségből s kihozza világosságra a vakhomályt.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Nagyra növeszti a nemzeteket s elveszíti, kiterjeszti a nemzeteket és elviszi.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Szívét veszi az ország népe fejeinek s eltévelyíti úttalan pusztaságban;
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 tapogatóznak sötétségben világosság nélkül, s eltévelyíti őket mint a részeget.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.