< תהילים 50 >

מזמור לאסף אל אלהים יהוה דבר ויקרא ארץ ממזרח שמש עד מבאו׃ 1
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
מציון מכלל יפי אלהים הופיע׃ 2
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
יבא אלהינו ואל יחרש אש לפניו תאכל וסביביו נשערה מאד׃ 3
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
יקרא אל השמים מעל ואל הארץ לדין עמו׃ 4
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
אספו לי חסידי כרתי בריתי עלי זבח׃ 5
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
ויגידו שמים צדקו כי אלהים שפט הוא סלה׃ 6
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
שמעה עמי ואדברה ישראל ואעידה בך אלהים אלהיך אנכי׃ 7
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
לא על זבחיך אוכיחך ועולתיך לנגדי תמיד׃ 8
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
לא אקח מביתך פר ממכלאתיך עתודים׃ 9
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
כי לי כל חיתו יער בהמות בהררי אלף׃ 10
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
ידעתי כל עוף הרים וזיז שדי עמדי׃ 11
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
אם ארעב לא אמר לך כי לי תבל ומלאה׃ 12
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
האוכל בשר אבירים ודם עתודים אשתה׃ 13
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
זבח לאלהים תודה ושלם לעליון נדריך׃ 14
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
וקראני ביום צרה אחלצך ותכבדני׃ 15
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
ולרשע אמר אלהים מה לך לספר חקי ותשא בריתי עלי פיך׃ 16
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
ואתה שנאת מוסר ותשלך דברי אחריך׃ 17
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
אם ראית גנב ותרץ עמו ועם מנאפים חלקך׃ 18
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
פיך שלחת ברעה ולשונך תצמיד מרמה׃ 19
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
תשב באחיך תדבר בבן אמך תתן דפי׃ 20
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
אלה עשית והחרשתי דמית היות אהיה כמוך אוכיחך ואערכה לעיניך׃ 21
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
בינו נא זאת שכחי אלוה פן אטרף ואין מציל׃ 22
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
זבח תודה יכבדנני ושם דרך אראנו בישע אלהים׃ 23
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< תהילים 50 >