< תהילים 50 >
מזמור לאסף אל אלהים יהוה דבר ויקרא ארץ ממזרח שמש עד מבאו׃ | 1 |
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
מציון מכלל יפי אלהים הופיע׃ | 2 |
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
יבא אלהינו ואל יחרש אש לפניו תאכל וסביביו נשערה מאד׃ | 3 |
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
יקרא אל השמים מעל ואל הארץ לדין עמו׃ | 4 |
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
אספו לי חסידי כרתי בריתי עלי זבח׃ | 5 |
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
ויגידו שמים צדקו כי אלהים שפט הוא סלה׃ | 6 |
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
שמעה עמי ואדברה ישראל ואעידה בך אלהים אלהיך אנכי׃ | 7 |
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
לא על זבחיך אוכיחך ועולתיך לנגדי תמיד׃ | 8 |
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
לא אקח מביתך פר ממכלאתיך עתודים׃ | 9 |
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
כי לי כל חיתו יער בהמות בהררי אלף׃ | 10 |
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
ידעתי כל עוף הרים וזיז שדי עמדי׃ | 11 |
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
אם ארעב לא אמר לך כי לי תבל ומלאה׃ | 12 |
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
האוכל בשר אבירים ודם עתודים אשתה׃ | 13 |
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
זבח לאלהים תודה ושלם לעליון נדריך׃ | 14 |
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
וקראני ביום צרה אחלצך ותכבדני׃ | 15 |
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
ולרשע אמר אלהים מה לך לספר חקי ותשא בריתי עלי פיך׃ | 16 |
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
ואתה שנאת מוסר ותשלך דברי אחריך׃ | 17 |
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
אם ראית גנב ותרץ עמו ועם מנאפים חלקך׃ | 18 |
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
פיך שלחת ברעה ולשונך תצמיד מרמה׃ | 19 |
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
תשב באחיך תדבר בבן אמך תתן דפי׃ | 20 |
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
אלה עשית והחרשתי דמית היות אהיה כמוך אוכיחך ואערכה לעיניך׃ | 21 |
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
בינו נא זאת שכחי אלוה פן אטרף ואין מציל׃ | 22 |
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
זבח תודה יכבדנני ושם דרך אראנו בישע אלהים׃ | 23 |
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”