< תהילים 44 >
למנצח לבני קרח משכיל אלהים באזנינו שמענו אבותינו ספרו לנו פעל פעלת בימיהם בימי קדם׃ | 1 |
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
אתה ידך גוים הורשת ותטעם תרע לאמים ותשלחם׃ | 2 |
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
כי לא בחרבם ירשו ארץ וזרועם לא הושיעה למו כי ימינך וזרועך ואור פניך כי רציתם׃ | 3 |
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
אתה הוא מלכי אלהים צוה ישועות יעקב׃ | 4 |
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
בך צרינו ננגח בשמך נבוס קמינו׃ | 5 |
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
כי לא בקשתי אבטח וחרבי לא תושיעני׃ | 6 |
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
כי הושעתנו מצרינו ומשנאינו הבישות׃ | 7 |
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
באלהים הללנו כל היום ושמך לעולם נודה סלה׃ | 8 |
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
אף זנחת ותכלימנו ולא תצא בצבאותינו׃ | 9 |
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
תשיבנו אחור מני צר ומשנאינו שסו למו׃ | 10 |
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
תתננו כצאן מאכל ובגוים זריתנו׃ | 11 |
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
תמכר עמך בלא הון ולא רבית במחיריהם׃ | 12 |
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
תשימנו חרפה לשכנינו לעג וקלס לסביבותינו׃ | 13 |
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
תשימנו משל בגוים מנוד ראש בל אמים׃ | 14 |
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
כל היום כלמתי נגדי ובשת פני כסתני׃ | 15 |
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
מקול מחרף ומגדף מפני אויב ומתנקם׃ | 16 |
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
כל זאת באתנו ולא שכחנוך ולא שקרנו בבריתך׃ | 17 |
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
לא נסוג אחור לבנו ותט אשרינו מני ארחך׃ | 18 |
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
כי דכיתנו במקום תנים ותכס עלינו בצלמות׃ | 19 |
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
אם שכחנו שם אלהינו ונפרש כפינו לאל זר׃ | 20 |
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
הלא אלהים יחקר זאת כי הוא ידע תעלמות לב׃ | 21 |
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
כי עליך הרגנו כל היום נחשבנו כצאן טבחה׃ | 22 |
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
עורה למה תישן אדני הקיצה אל תזנח לנצח׃ | 23 |
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
למה פניך תסתיר תשכח ענינו ולחצנו׃ | 24 |
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
כי שחה לעפר נפשנו דבקה לארץ בטננו׃ | 25 |
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
קומה עזרתה לנו ופדנו למען חסדך׃ | 26 |
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.