< תהילים 25 >

לדוד אליך יהוה נפשי אשא׃ 1
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
אלהי בך בטחתי אל אבושה אל יעלצו איבי לי׃ 2
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
גם כל קויך לא יבשו יבשו הבוגדים ריקם׃ 3
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
דרכיך יהוה הודיעני ארחותיך למדני׃ 4
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
הדריכני באמתך ולמדני כי אתה אלהי ישעי אותך קויתי כל היום׃ 5
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
זכר רחמיך יהוה וחסדיך כי מעולם המה׃ 6
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
חטאות נעורי ופשעי אל תזכר כחסדך זכר לי אתה למען טובך יהוה׃ 7
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
טוב וישר יהוה על כן יורה חטאים בדרך׃ 8
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
ידרך ענוים במשפט וילמד ענוים דרכו׃ 9
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
כל ארחות יהוה חסד ואמת לנצרי בריתו ועדתיו׃ 10
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
למען שמך יהוה וסלחת לעוני כי רב הוא׃ 11
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
מי זה האיש ירא יהוה יורנו בדרך יבחר׃ 12
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
נפשו בטוב תלין וזרעו יירש ארץ׃ 13
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
סוד יהוה ליראיו ובריתו להודיעם׃ 14
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
עיני תמיד אל יהוה כי הוא יוציא מרשת רגלי׃ 15
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
פנה אלי וחנני כי יחיד ועני אני׃ 16
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
צרות לבבי הרחיבו ממצוקותי הוציאני׃ 17
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
ראה עניי ועמלי ושא לכל חטאותי׃ 18
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
ראה אויבי כי רבו ושנאת חמס שנאוני׃ 19
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
שמרה נפשי והצילני אל אבוש כי חסיתי בך׃ 20
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
תם וישר יצרוני כי קויתיך׃ 21
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
פדה אלהים את ישראל מכל צרותיו׃ 22
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< תהילים 25 >