< תהילים 116 >

אהבתי כי ישמע יהוה את קולי תחנוני׃ 1
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
כי הטה אזנו לי ובימי אקרא׃ 2
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
אפפוני חבלי מות ומצרי שאול מצאוני צרה ויגון אמצא׃ (Sheol h7585) 3
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
ובשם יהוה אקרא אנה יהוה מלטה נפשי׃ 4
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
חנון יהוה וצדיק ואלהינו מרחם׃ 5
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
שמר פתאים יהוה דלותי ולי יהושיע׃ 6
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
שובי נפשי למנוחיכי כי יהוה גמל עליכי׃ 7
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
כי חלצת נפשי ממות את עיני מן דמעה את רגלי מדחי׃ 8
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
אתהלך לפני יהוה בארצות החיים׃ 9
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
האמנתי כי אדבר אני עניתי מאד׃ 10
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
אני אמרתי בחפזי כל האדם כזב׃ 11
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
מה אשיב ליהוה כל תגמולוהי עלי׃ 12
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
כוס ישועות אשא ובשם יהוה אקרא׃ 13
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
נדרי ליהוה אשלם נגדה נא לכל עמו׃ 14
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
יקר בעיני יהוה המותה לחסידיו׃ 15
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
אנה יהוה כי אני עבדך אני עבדך בן אמתך פתחת למוסרי׃ 16
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
לך אזבח זבח תודה ובשם יהוה אקרא׃ 17
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
נדרי ליהוה אשלם נגדה נא לכל עמו׃ 18
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
בחצרות בית יהוה בתוככי ירושלם הללו יה׃ 19
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< תהילים 116 >