< תהילים 116 >
אהבתי כי ישמע יהוה את קולי תחנוני׃ | 1 |
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
כי הטה אזנו לי ובימי אקרא׃ | 2 |
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
אפפוני חבלי מות ומצרי שאול מצאוני צרה ויגון אמצא׃ (Sheol ) | 3 |
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
ובשם יהוה אקרא אנה יהוה מלטה נפשי׃ | 4 |
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
חנון יהוה וצדיק ואלהינו מרחם׃ | 5 |
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
שמר פתאים יהוה דלותי ולי יהושיע׃ | 6 |
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
שובי נפשי למנוחיכי כי יהוה גמל עליכי׃ | 7 |
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
כי חלצת נפשי ממות את עיני מן דמעה את רגלי מדחי׃ | 8 |
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
אתהלך לפני יהוה בארצות החיים׃ | 9 |
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
האמנתי כי אדבר אני עניתי מאד׃ | 10 |
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
אני אמרתי בחפזי כל האדם כזב׃ | 11 |
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
מה אשיב ליהוה כל תגמולוהי עלי׃ | 12 |
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
כוס ישועות אשא ובשם יהוה אקרא׃ | 13 |
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
נדרי ליהוה אשלם נגדה נא לכל עמו׃ | 14 |
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
יקר בעיני יהוה המותה לחסידיו׃ | 15 |
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
אנה יהוה כי אני עבדך אני עבדך בן אמתך פתחת למוסרי׃ | 16 |
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
לך אזבח זבח תודה ובשם יהוה אקרא׃ | 17 |
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
נדרי ליהוה אשלם נגדה נא לכל עמו׃ | 18 |
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
בחצרות בית יהוה בתוככי ירושלם הללו יה׃ | 19 |
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.