< תהילים 110 >
לדוד מזמור נאם יהוה לאדני שב לימיני עד אשית איביך הדם לרגליך׃ | 1 |
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
מטה עזך ישלח יהוה מציון רדה בקרב איביך׃ | 2 |
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
עמך נדבת ביום חילך בהדרי קדש מרחם משחר לך טל ילדתיך׃ | 3 |
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
נשבע יהוה ולא ינחם אתה כהן לעולם על דברתי מלכי צדק׃ | 4 |
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
אדני על ימינך מחץ ביום אפו מלכים׃ | 5 |
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
ידין בגוים מלא גויות מחץ ראש על ארץ רבה׃ | 6 |
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
מנחל בדרך ישתה על כן ירים ראש׃ | 7 |
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.