< תהילים 110 >

לדוד מזמור נאם יהוה לאדני שב לימיני עד אשית איביך הדם לרגליך׃ 1
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
מטה עזך ישלח יהוה מציון רדה בקרב איביך׃ 2
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
עמך נדבת ביום חילך בהדרי קדש מרחם משחר לך טל ילדתיך׃ 3
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
נשבע יהוה ולא ינחם אתה כהן לעולם על דברתי מלכי צדק׃ 4
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
אדני על ימינך מחץ ביום אפו מלכים׃ 5
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
ידין בגוים מלא גויות מחץ ראש על ארץ רבה׃ 6
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
מנחל בדרך ישתה על כן ירים ראש׃ 7
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< תהילים 110 >