< חזוֹן יוֹחָנָן 5 >

ראיתי לימין היושב על הכסא מגילה כתובה בפנים ובחוץ וחתומה בשבעה חותמות. 1
Sa’an nan na ga a hannun damar wannan wanda yake zaune a kursiyin naɗaɗɗen littafi da rubutu a ciki da wajensa an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
מלאך גיבור הופיע וקרא בקול גדול:”מי ראוי לשבור את החותמות ולפתוח את המגילה?“ 2
Na kuma ga wani babban mala’ika yana shela da babbar murya cewa, “Wa ya cancanta yă ɓalle hatiman nan yă kuma buɗe naɗaɗɗen littafin?”
ולא נמצא איש בשמים, בארץ או מבין המתים אשר היה מסוגל לפתוח את המגילה או להביט בכתוב. 3
Amma ba wani a sama ko a ƙasa ko a ƙarƙashin ƙasan da ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin ko ma yă duba cikinsa.
פרצתי בבכי מר, כי איש לא נמצא ראוי לפתוח את המגילה ולקרוא בה. 4
Na yi ta kuka domin ba a iya samun wanda ya cancanta yă buɗe naɗaɗɗen littafin ko yă duba cikinsa ba.
אך אחד מעשרים־וארבעה הזקנים אמר אלי:”אל תבכה. ראה, האריה משבט יהודה ושורש דויד ניצח, והוכיח את עצמו ראוי לשבור את החותמות ולפתוח את המגילה.“ 5
Sai ɗaya daga cikin dattawan ya ce mini, “Kada ka yi kuka! Duba, Zakin kabilar Yahuda, da kuma Tushen Dawuda ya ci nasara. Ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin da hatimansa bakwai.”
הבטתי במרכז כסא־המלכות, שמוקף בארבע החיות ובעשרים־וארבעה הזקנים, וראיתי שה שעליו פצעים וחבורות אשר גרמו פעם למותו. לשה היו שבע קרניים ושבע עיניים, שהן שבע רוחות האלוהים שנשלחות אל כל קצווי העולם. 6
Sa’an nan na ga Ɗan Rago, yana kamar an yanka, tsaye a tsakiyar kursiyin, halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan an sun kewaye shi. Yana da ƙahoni bakwai da idanu bakwai, waɗanda suke ruhohi bakwai na Allah da aka aika cikin dukan duniya.
השה בא ולקח את המגילה מימינו של היושב על כיסא המלכות. 7
Ya zo ya karɓi naɗaɗɗen littafin daga hannun dama na wannan wanda yake zaune a kursiyin.
בלקחו את המגילה השתחוו לפניו ארבע החיות ועשרים־וארבעה הזקנים. כל אחד מהזקנים אחז כינור וקערת זהב מלאה קטורת, אשר היא תפילת בני־האלוהים הקדושים. 8
Bayan ya karɓa, sai halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi ƙasa a gaban Ɗan Ragon. Kowannensu yana da garaya kuma suna riƙe da kaskon zinariya cike da turare, waɗanda suke addu’o’in tsarkaka.
הם שרו שיר חדש, ואלו מילותיו:”ראוי אתה לקחת את המגילה ולפתוח את חותמיה, כי אתה נשחטת, ובדמך קנית לאלוהים את בניו מכל עם, גזע ולשון. 9
Suka rera sabuwar waƙa, “Ka cancanci ka karɓi naɗaɗɗen littafin ka kuma buɗe hatimansa, domin an kashe ka, da jininka kuma ka sayi mutane wa Allah, daga kowace kabila da harshe da mutane da kuma al’umma.
ממלכת כוהנים לאלוהינו עשית אותם, והם ימלכו על הארץ.“ 10
Ka mai da su masarauta da kuma firistoci, don su yi wa Allahnmu hidima, kuma za su yi mulki a duniya.”
לאחר מכן שמעתי בחיזיון קול מלאכים רבים סביב כסא המלכות, ארבע החיות והזקנים. 11
Sai na duba na kuma ji muryar mala’iku masu yawa, yawansu kuwa ya kai dubu dubbai, da kuma dubu goma sau dubu goma. Suka kewaye kursiyin da halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan.
הם שרו שירה אדירה:”ראוי השה הטבוח לקבל עוז, עושר וחכמה, גבורה והדר, כבוד וברכה.“ 12
Da babbar murya suka rera, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe, don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”
וכל בריה בשמים, בארץ, מתחת לארץ ובים, שמעתי קוראים:”ליושב על הכסא ולשה הברכה וההדר והעוז, לעולם ועד!“ (aiōn g165) 13
Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn g165)
ארבע החיות אמרו:”אמן!“ועשרים וארבעה הזקנים נפלו על פניהם והשתחוו לו. 14
Sai halittu huɗun nan masu rai suka ce, “Amin”, dattawan kuma suka fāɗi suka yi sujada.

< חזוֹן יוֹחָנָן 5 >