< לוּקָס 1 >
תאופילוס היקר, אנשים רבים כבר כתבו על הדברים שהתרחשו בינינו, | 1 |
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
על־פי סיפוריהם של תלמידי ישוע ושל עדי ראייה אחרים. | 2 |
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
גם אני חקרתי היטב את התרחשות הדברים מתחילתם, והחלטתי כי טוב שאכתוב לך אותם לפי סדר העניינים, | 3 |
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
כדי שיהיה לך מידע מדויק על הנושא שלמדת. | 4 |
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
בימי הורדוס מלך יהודה היה בארץ כהן בשם זכריה, אשר היה שייך למחלקת אביה – ממשרתי בית־המקדש. גם אשתו אלישבע הייתה ממשפחה כוהנית. | 5 |
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
זכריה ואלישבע היו אנשים צדיקים, אשר אהבו את ה׳ ושמרו את כל מצוותיו וחוקותיו. | 6 |
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
אולם לא היו להם ילדים, כי אלישבע הייתה עקרה, ושניהם כבר היו זקנים. | 7 |
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
יום אחד, כאשר הייתה מחלקתו של זכריה בתורנות בבית־המקדש, נפל בגורלו להיכנס אל היכל ה׳ ולהקטיר קטורת. | 8 |
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
בינתיים עמד כל העם בחוץ והתפלל, כנהוג בעת הקטרת הקטורת. | 10 |
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
לפתע נראה מלאך ה׳ אל זכריה מימין למזבח הקטורת. | 11 |
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
”אל תירא, זכריה“, הרגיע אותו המלאך.”באתי לבשר לך שאלוהים שמע את תפילתך, ושאשתך אלישבע תלד לך בן! עליך לקרוא לו’יוחנן‘. | 13 |
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
לידתו תביא לכם שמחה ואושר, ואנשים רבים ישמחו יחד אתכם, | 14 |
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
כי ה׳ הועיד אותו לגדולות. עליו להינזר מיין ומשקאות חריפים, והוא יימלא ברוח הקודש מעת לידתו. | 15 |
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
יוחנן ישיב רבים מעם ישראל אל ה׳ אלוהיהם. | 16 |
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
הוא ילך לפני ה׳ ברוחו ובגבורתו של אליהו הנביא, ישלים בין אבות לבנים, וישיב את המרדנים לדרך הצדקה והתבונה. אכן, הוא יכין את העם לבואו של האדון.“ | 17 |
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
”כיצד אדע שדבריך נכונים?“שאל זכריה.”הלא אדם זקן אני, וגם אשתי כבר זקנה.“ | 18 |
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
”אני המלאך גבריאל!“השיב המלאך.”אני עומד לפני אלוהים, והוא אשר שלח אותי לבשר לך את ההודעה הזאת. | 19 |
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
דע לך כי כל אשר אמרתי יתקיים בבוא הזמן, אולם מאחר שלא האמנת לדברי, לא תוכל להוציא מילה מפיך מרגע זה ועד שיתקיימו דברי!“ | 20 |
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
האנשים אשר התפללו בחוץ המתינו בינתיים לזכריה, ולא הבינו מדוע התעכב. | 21 |
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
לבסוף, כשיצא זכריה החוצה הוא לא יכול היה לדבר אל העם, אולם מסימני ידיים הבינו האנשים שראה חזיון. | 22 |
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
זכריה נשאר בבית־המקדש עד תום ימי התורנות של מחלקתו, ולאחר מכן שב לביתו. | 23 |
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
כעבור זמן קצר הרתה אלישבע אשתו והסתתרה מעיני הציבור כחמישה חודשים. | 24 |
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
”מה טוב הוא אלוהים!“קראה אלישבע בשמחה רבה.”ברחמיו הרבים הוא הסיר את חרפת עקרותי!“ | 25 |
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
בחודש השישי להריונה של אלישבע שלח אלוהים את המלאך גבריאל אל העיר נצרת שבגליל, | 26 |
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
אל נערה בתולה בשם מרים, ארוסתו של יוסף משושלת בית־דוד. | 27 |
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
גבריאל נגלה אל מרים ואמר לה:”שלום לך, אשת חן, ה׳ עמך!“ | 28 |
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
מרים נבהלה לרגע; דברי המלאך הביכו אותה, והיא ניסתה לנחש בלבה למה הוא התכוון. | 29 |
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
”אל תפחדי, מרים, “הרגיע אותה המלאך,”כי מצאת חן בעיני אלוהים והוא החליט לברך אותך. | 30 |
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
בעוד זמן קצר תיכנסי להריון ותלדי בן. בשם’ישוע‘תקראי לו. | 31 |
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
הוא יהיה רם־מעלה וייקרא בן־אלוהים. ה׳ ייתן לו את כסא דוד אביו, | 32 |
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
והוא ימלוך על עם־ישראל לעולם ועד; מלכותו לא תסתיים לעולם.“ (aiōn ) | 33 |
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
”כיצד אוכל ללדת?“שאלה מרים בתמיהה.”הרי אני בתולה!“ | 34 |
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
השיב לה המלאך:”רוח הקודש תבוא אליך, וגבורת אלוהים תצל עליך. משום כך הבן הקדוש שייוולד ייקרא בן־אלוהים.“ | 35 |
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
המלאך המשיך:”לפני שישה חודשים נכנסה קרובתך הזקנה אלישבע להריון – כן, זו ששכנותיה קראו לה’העקרה‘– וגם היא תלד בן! | 36 |
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
כי אין דבר בלתי אפשרי לאלוהים“. | 37 |
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
”הנני שפחתך, אדוני, “אמרה מרים בענווה,”ואני מוכנה לעשות את כל אשר יאמר לי. אמן שיתקיימו דבריך.“לאחר מכן נעלם המלאך. | 38 |
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
כעבור ימים אחדים מיהרה מרים אל הרי יהודה, אל ביתו של זכריה, ובהיכנסה אל הבית ברכה את אלישבע לשלום. | 39 |
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
לשמע ברכתה של מרים התנועע התינוק בבטנה של אלישבע, והיא נמלאה ברוח הקודש. | 41 |
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
”ברוכה את בנשים, מרים, וברוך תינוקך!“פרצה אלישבע בקריאת שמחה. | 42 |
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
”מדוע זכיתי בכבוד הגדול שאם אדוני באה לבקר אותי? | 43 |
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
התינוק בבטני התנועע בשמחה לשמע קול ברכתך! | 44 |
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
אלוהים ברך אותך בצורה נפלאה כזאת משום שהאמנת כי יקיים את דבריו.“ | 45 |
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
השיבה מרים:”ברכי נפשי את ה׳; | 46 |
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
אגיל ואשמח באלוהים מושיעי! | 47 |
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
כי עשה חסד עם שפחתו, ומעתה יברכוני כל הדורות. | 48 |
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
גדולות ונפלאות עשה עמי אל שדי, קדוש שמו. | 49 |
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
מדור לדור הוא מעניק את חסדו ורחמיו לכל היראים אותו. | 50 |
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
בזרוע נטויה עשה מעשי גבורה, הפר מזימות גאים ורשעים, | 51 |
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
והוריד שליטים מכיסאם. אולם את השפלים והנחותים הוא רומם! | 52 |
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
את העניים האכיל ואת העשירים הרעיב! | 53 |
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
אלוהים תמך בעבדו ישראל, ולא שכח כי הבטיח לאבותינו – לאברהם ולזרעו – לרחם על ישראל לעולם ועד!“ (aiōn ) | 54 |
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
מרים נשארה אצל אלישבע כשלושה חודשים, ולאחר מכן חזרה לביתה. | 56 |
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
בינתיים תמו ימי הריונה של אלישבע והיא ילדה בן. | 57 |
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
השמועה על החסד שעשה איתה ה׳ התפשטה עד מהרה בין שכניה וקרובי משפחתה, וכולם שמחו בשמחתה. | 58 |
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
ביום השמיני להולדת התינוק התכנסו השכנים והקרובים לטקס ברית־המילה. האורחים היו בטוחים שהתינוק ייקרא”זכריה“– על שם אביו, | 59 |
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
אולם אלישבע אמרה:”לא, שם התינוק יוחנן!“ | 60 |
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
”יוחנן?“התפלאו האורחים.”אבל אין במשפחתך אף אחד בשם הזה“. | 61 |
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
הם פנו אל זכריה (שעדיין לא היה מסוגל לדבר), ושאלו אותו בתנועות ידיים וברמזים כיצד ייקרא התינוק. | 62 |
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
זכריה ביקש בתנועות ידיים שיביאו לו לוח, וכתב עליו:”שם הילד יוחנן“. | 63 |
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
באותו רגע חזר אליו כושר הדיבור והוא החל לברך את אלוהים. | 64 |
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
כל השכונה נמלאה יראת כבוד, והדבר היה נושא לשיחה בכל הרי יהודה. | 65 |
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
כל השומעים התרשמו עמוקות ואמרו:”מעניין למה נועד הילד הזה.“כי היה ברור להם שאלוהים איתו. | 66 |
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
לאחר מכן נמלא זכריה אביו רוח הקודש וניבא את הנבואה הבאה: | 67 |
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
”ברוך ה׳ אלוהי ישראל, כי פנה אל עמו, הודיע ופדה אותו. | 68 |
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
ה׳ שלח לנו מושיע גיבור משושלת בית דוד עבדו – | 69 |
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
כפי שהבטיח לנו בפי נביאיו הקדושים עוד לפני זמן רב – (aiōn ) | 70 |
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
כדי להצילנו מיד כל אויבינו ושונאינו. | 71 |
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
אלוהים יעשה חסד עם אבותינו ויזכור את בריתו | 72 |
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
ואת שבועתו לאברהם אבינו: | 73 |
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
להצילנו מיד אויבינו, ולהעניק לנו את הזכות לשרתו כל ימי חיינו בקדושה, ובצדקה וללא פחד.“ | 74 |
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
”ואתה, ילדי הקטן, תיקרא נביא לאל עליון, כי תלך לפני האדון ותפנה לו את הדרך. | 76 |
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
אתה תלמד את בני־ישראל כיצד הם יכולים להיוושע על־ידי סליחת חטאיהם. | 77 |
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
בזכות אהבתו, רחמיו וטוב־לבו של אלוהים יזרח עלינו אור ממרום, | 78 |
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
כדי להאיר לשרויים במוות ובחשכה, וכדי להוביל את רגלינו אל דרך השלום.“ | 79 |
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
הילד גדל, התחזק והתחשל באופיו. הוא התגורר במדבר עד שהגיע המועד להתחיל את שליחותו אל עם־ישראל. | 80 |
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.