< ג'ון 5 >

כעבור זמן מה חזר ישוע לירושלים לרגל אחד החגים. 1
Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
ליד שער הצאן בירושלים הייתה ברכה שנקראת בעברית”בית־חסדא“, וסביבה חמישה רציפים. 2
To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
על רציפים אלה שכבו חולים רבים, עיוורים, פיסחים, משותקים וכדומה (כשהם מחכים שהמים יסערו, 3
A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
כי מדי פעם ירד מלאך ה׳ אל הברכה והסעיר את המים, והחולה הראשון שנכנס אל המים לאחר מכן נרפא). 4
בין החולים הרבים היה אדם שסבל ממחלתו במשך שלושים ושמונה שנים. 5
Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
ישוע הביט באיש ומיד ידע את משך מחלתו.”אתה רוצה להירפא?“שאל ישוע. 6
Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
”איני יכול!“השיב האיש בייאוש.”אין מי שיעזור לי להיכנס למים בעת הסערה, ובזמן שאני מנסה להיכנס לברכה בכוחות עצמי, מישהו זריז ממני מקדים אותי ונכנס למים לפני.“ 7
Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
”קום, קפל את האלונקה שלך והתהלך!“פקד ישוע. 8
Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
האיש נרפא מיד, עמד על רגליו, קיפל את האלונקה והלך לדרכו. מאחר שהמעשה התרחש בשבת, 9
Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
לא מצא הדבר חן בעיני היהודים.”אסור לך לשאת את האלונקה, כי שבת היום!“קראו לעבר הנרפא. 10
saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
”האיש שריפא אותי פקד עלי לקפל את האלונקה וללכת“, ענה האיש. 11
Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
”מיהו האיש הזה?“שאלו. 12
Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
אך הנרפא לא יכול היה להשיב להם, כי הוא בעצמו לא ידע מי הוא כי בינתיים נעלם ישוע בקהל הרב שהיה במקום. 13
Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
מאוחר יותר פגש ישוע את הנרפא בבית־המקדש ואמר לו:”עתה, לאחר שהבראת, אל תמשיך לחטוא, פן יבוא עליך משהו יותר רע.“ 14
Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
האיש הלך מהר וסיפר ליהודים כי ישוע הוא זה שריפא אותו. 15
Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
ואז החלו מנהיגי היהודים לרדוף את ישוע, מפני שחילל את השבת. 16
To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
אבל ישוע אמר להם:”אבי לא הפסיק לעבוד עד עתה, ואני נוהג כמוהו!“ 17
Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
דבריו עוררו עוד יותר את חמת מנהיגי היהודים, והם רצו להרגו לא רק על שום שחילל את השבת, אלא גם על שקרא לאלוהים”אביו“, ובכך השווה את עצמו לאלוהים. 18
Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
”הבן אינו יכול לעשות דבר בעצמו, “אמר ישוע,”הוא עושה רק מה שראה את אביו עושה, ובאותה דרך. 19
Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
כי האב אוהב את בנו ומלמד אותו את כל מעשיו, ואפילו מלמדו לעשות מעשים גדולים יותר מריפוי האיש הזה. אתם יודעים מדוע? כדי שתתפלאו ותשתוממו! 20
Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
הבן אף יקים מהמתים את מי שירצה, ממש כפי שעושה האב. 21
Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
האב לא ישפוט איש – הוא נתן לבנו את סמכות המשפט, כדי שכולם יכבדו את הבן כפי שהם מכבדים את האב. 22
Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
מי שאינו מכבד את הבן אינו מכבד גם את האב אשר שלח אותו. 23
don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
”אני מבטיח לכם שכל השומע את דברי ומאמין באלוהים אשר שלח אותי, יחיה חיי נצח ולא יישפט על חטאיו לעולם, משום שהוא כבר עבר מהמוות לחיים. (aiōnios g166) 24
“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
אני מבטיח לכם, יגיע הזמן, ולמעשה הוא כבר הגיע, שהמתים ישמעו את קולו של בן־האלוהים – וכל השומעים יחיו. 25
Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
כשם שלאב עצמו יש כוח המעניק חיים, כך גם לבן יש אותו כוח, שהוא מתנת האב. 26
Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
כבן־האדם יש לו זכות וסמכות לשפוט את חטאיהם של כל בני־האדם. 27
Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
אל תתפלאו על כך, כי יבוא הזמן שכל המתים ישמעו בקבריהם את קולו של בן האלוהים, 28
“Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
והם יקומו מקבריהם – עושי הטוב לחיי נצח, ועושי הרע למשפט. 29
su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
”איני שופט איש לפני התייעצות עם אבי; אני שופט רק לפי מה שהוא אומר לי. משפטי ישר וצודק, כי איני מבקש את טובת עצמי, אלא את רצון אבי שבשמים אשר שלחני. 30
Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
”אם אני מעיד על עצמי, תאמרו שעדותי אינה מהימנה. 31
“In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
אולם מישהו אחר מעיד עלי – יוחנן המטביל, ואני יודע שאפשר לסמוך על דבריו. 32
Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
אתם שלחתם את אנשיכם אל יוחנן כדי להקשיב לדבריו, ויוחנן אמר את האמת. 33
“Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
אל תחשבו שאני זקוק לעדות בני־אדם; אני מספר לכם כל זאת רק כדי שתאמינו ותיוושעו. 34
Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
”יוחנן הפיץ אור כנר דולק כדי להאיר לכם את הדרך, ולזמן קצר אף שמחתם להתענג על האור הזה. 35
Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
ברם יש לי עדות גדולה יותר מעדותו של יוחנן: המעשים שאני עושה. אלוהים אבי הטיל עלי לעשות את המעשים האלה, והם מוכיחים שהוא שלח אותי. 36
“Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
האב עצמו מעיד עלי, למרות שמעולם לא שמעתם את קולו, ואת מראהו לא ראיתם. 37
Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
אולם דברו אינו שוכן בכם כלל, כי אתם מסרבים להאמין שאני שליחו. 38
maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
”אתם דורשים בכתובים מתוך תקווה למצוא בהם חיי נצח, אך הכתובים מצביעים עלי! (aiōnios g166) 39
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
למרות זאת אינכם רוצים לבוא אלי כדי שאעניק לכם חיי נצח. 40
duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
”איני לוקח כבוד ושבחים מבני־אדם ואיני דואג לדעתכם עלי, 41
“Ni ba na neman yabon mutane,
אבל אני רוצה לומר לכם שאינכם אוהבים את אלוהים. 42
na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
אני באתי בשם אבי ולא קיבלתם אותי; אך אם יבוא מישהו אחר בשם עצמו, כן תקבלו אותו. 43
Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
אין פלא שאינכם מאמינים, שכן אתם מבקשים כבוד איש מרעהו, וכלל אינכם דואגים לכבוד שחולק אלוהים. 44
Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
”אל תחשבו שאטען עליכם לפני אבי. משה רבנו – שבו אתם מאמינים – הוא הטוען עליכם! 45
“Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
אילו האמנתם למשה הייתם מאמינים גם לי, שהרי הוא כתב עלי. 46
Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
ואם אינכם מאמינים למה שכתב משה, איני מתפלא שאינכם מאמינים לדברי.“ 47
Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”

< ג'ון 5 >