< תְהִלִּים 132 >
שִׁ֗יר הַֽמַּ֫עֲלֹ֥ות זְכֹור־יְהוָ֥ה לְדָוִ֑ד אֵ֝ת כָּל־עֻנֹּותֹֽו׃ | 1 |
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
אֲשֶׁ֣ר נִ֭שְׁבַּע לַיהוָ֑ה נָ֝דַ֗ר לַאֲבִ֥יר יַעֲקֹֽב׃ | 2 |
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
אִם־אָ֭בֹא בְּאֹ֣הֶל בֵּיתִ֑י אִם־אֶ֝עֱלֶ֗ה עַל־עֶ֥רֶשׂ יְצוּעָֽי׃ | 3 |
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
אִם־אֶתֵּ֣ן שְׁנַ֣ת לְעֵינָ֑י לְֽעַפְעַפַּ֥י תְּנוּמָֽה׃ | 4 |
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
עַד־אֶמְצָ֣א מָ֭קֹום לַיהוָ֑ה מִ֝שְׁכָּנֹ֗ות לַאֲבִ֥יר יַעֲקֹֽב׃ | 5 |
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
הִנֵּֽה־שְׁמַֽעֲנ֥וּהָ בְאֶפְרָ֑תָה מְ֝צָאנ֗וּהָ בִּשְׂדֵי־יָֽעַר׃ | 6 |
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
נָבֹ֥ואָה לְמִשְׁכְּנֹותָ֑יו נִ֝שְׁתַּחֲוֶ֗ה לַהֲדֹ֥ם רַגְלָֽיו׃ | 7 |
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
קוּמָ֣ה יְ֭הוָה לִמְנוּחָתֶ֑ךָ אַ֝תָּ֗ה וַאֲרֹ֥ון עֻזֶּֽךָ׃ | 8 |
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
כֹּהֲנֶ֥יךָ יִלְבְּשׁוּ־צֶ֑דֶק וַחֲסִידֶ֥יךָ יְרַנֵּֽנוּ׃ | 9 |
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
בַּ֭עֲבוּר דָּוִ֣ד עַבְדֶּ֑ךָ אַל־תָּ֝שֵׁ֗ב פְּנֵ֣י מְשִׁיחֶֽךָ׃ | 10 |
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
נִשְׁבַּֽע־יְהוָ֨ה ׀ לְדָוִ֡ד אֱמֶת֮ לֹֽא־יָשׁ֪וּב מִ֫מֶּ֥נָּה מִפְּרִ֥י בִטְנְךָ֑ אָ֝שִׁ֗ית לְכִסֵּא־לָֽךְ׃ | 11 |
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
אִֽם־יִשְׁמְר֬וּ בָנֶ֨יךָ ׀ בְּרִיתִי֮ וְעֵדֹתִ֥י זֹ֗ו אֲלַ֫מְּדֵ֥ם גַּם־בְּנֵיהֶ֥ם עֲדֵי־עַ֑ד יֵ֝שְׁב֗וּ לְכִסֵּא־לָֽךְ׃ | 12 |
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
כִּֽי־בָחַ֣ר יְהוָ֣ה בְּצִיֹּ֑ון אִ֝וָּ֗הּ לְמֹושָׁ֥ב לֹֽו׃ | 13 |
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
זֹאת־מְנוּחָתִ֥י עֲדֵי־עַ֑ד פֹּֽה־אֵ֝שֵׁ֗ב כִּ֣י אִוִּתִֽיהָ׃ | 14 |
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
צֵ֭ידָהּ בָּרֵ֣ךְ אֲבָרֵ֑ךְ אֶ֝בְיֹונֶ֗יהָ אַשְׂבִּ֥יעַֽ לָֽחֶם׃ | 15 |
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
וְֽ֭כֹהֲנֶיהָ אַלְבִּ֣ישׁ יֶ֑שַׁע וַ֝חֲסִידֶ֗יהָ רַנֵּ֥ן יְרַנֵּֽנוּ׃ | 16 |
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
שָׁ֤ם אַצְמִ֣יחַ קֶ֣רֶן לְדָוִ֑ד עָרַ֥כְתִּי נֵ֝֗ר לִמְשִׁיחִֽי׃ | 17 |
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
אֹ֭ויְבָיו אַלְבִּ֣ישׁ בֹּ֑שֶׁת וְ֝עָלָ֗יו יָצִ֥יץ נִזְרֹֽו׃ | 18 |
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”