< אִיּוֹב 20 >
וַ֭יַּעַן צֹפַ֥ר הַנַּֽעֲמָתִ֗י וַיֹּאמַֽר׃ | 1 |
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
לָ֭כֵן שְׂעִפַּ֣י יְשִׁיב֑וּנִי וּ֝בַעֲב֗וּר ח֣וּשִׁי בִֽי׃ | 2 |
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
מוּסַ֣ר כְּלִמָּתִ֣י אֶשְׁמָ֑ע וְ֝ר֗וּחַ מִֽבִּינָתִ֥י יַעֲנֵֽנִי׃ | 3 |
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
הֲזֹ֣את יָ֭דַעְתָּ מִנִּי־עַ֑ד מִנִּ֤י שִׂ֖ים אָדָ֣ם עֲלֵי־אָֽרֶץ׃ | 4 |
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
כִּ֤י רִנְנַ֣ת רְ֭שָׁעִים מִקָּרֹ֑וב וְשִׂמְחַ֖ת חָנֵ֣ף עֲדֵי־רָֽגַע׃ | 5 |
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
אִם־יַעֲלֶ֣ה לַשָּׁמַ֣יִם שִׂיאֹ֑ו וְ֝רֹאשֹׁ֗ו לָעָ֥ב יַגִּֽיעַ׃ | 6 |
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
כְּֽ֭גֶלֲלֹו לָנֶ֣צַח יֹאבֵ֑ד רֹ֝אָ֗יו יֹאמְר֥וּ אַיֹּֽו׃ | 7 |
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
כַּחֲלֹ֣ום יָ֭עוּף וְלֹ֣א יִמְצָא֑וּהוּ וְ֝יֻדַּ֗ד כְּחֶזְיֹ֥ון לָֽיְלָה׃ | 8 |
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
עַ֣יִן שְׁ֭זָפַתּוּ וְלֹ֣א תֹוסִ֑יף וְלֹא־עֹ֝֗וד תְּשׁוּרֶ֥נּוּ מְקֹומֹֽו׃ | 9 |
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
בָּ֭נָיו יְרַצּ֣וּ דַלִּ֑ים וְ֝יָדָ֗יו תָּשֵׁ֥בְנָה אֹונֹֽו׃ | 10 |
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
עַ֭צְמֹותָיו מָלְא֣וּ עֲלוּמֹו (עֲלוּמָ֑יו) וְ֝עִמֹּ֗ו עַל־עָפָ֥ר תִּשְׁכָּֽב׃ | 11 |
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
אִם־תַּמְתִּ֣יק בְּפִ֣יו רָעָ֑ה יַ֝כְחִידֶ֗נָּה תַּ֣חַת לְשֹׁונֹֽו׃ | 12 |
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
יַחְמֹ֣ל עָ֭לֶיהָ וְלֹ֣א יַֽעַזְבֶ֑נָּה וְ֝יִמְנָעֶ֗נָּה בְּתֹ֣וךְ חִכֹּֽו׃ | 13 |
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
לַ֭חְמֹו בְּמֵעָ֣יו נֶהְפָּ֑ךְ מְרֹורַ֖ת פְּתָנִ֣ים בְּקִרְבֹּֽו׃ | 14 |
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
חַ֣יִל בָּ֭לַע וַיְקִאֶ֑נּוּ מִ֝בִּטְנֹ֗ו יֹֽורִשֶׁ֥נּוּ אֵֽל׃ | 15 |
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
רֹאשׁ־פְּתָנִ֥ים יִינָ֑ק תַּֽ֝הַרְגֵ֗הוּ לְשֹׁ֣ון אֶפְעֶֽה׃ | 16 |
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
אַל־יֵ֥רֶא בִפְלַגֹּ֑ות נַהֲרֵ֥י נַ֝חֲלֵ֗י דְּבַ֣שׁ וְחֶמְאָֽה׃ | 17 |
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
מֵשִׁ֣יב יָ֭גָע וְלֹ֣א יִבְלָ֑ע כְּחֵ֥יל תְּ֝מוּרָתֹ֗ו וְלֹ֣א יַעֲלֹֽס׃ | 18 |
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
כִּֽי־רִ֭צַּץ עָזַ֣ב דַּלִּ֑ים בַּ֥יִת גָּ֝זַ֗ל וְלֹ֣א יִבֶנֵֽהוּ׃ | 19 |
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
כִּ֤י ׀ לֹא־יָדַ֣ע שָׁלֵ֣ו בְּבִטְנֹ֑ו בַּ֝חֲמוּדֹ֗ו לֹ֣א יְמַלֵּֽט׃ | 20 |
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
אֵין־שָׂרִ֥יד לְאָכְלֹ֑ו עַל־כֵּ֝֗ן לֹא־יָחִ֥יל טוּבֹֽו׃ | 21 |
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
בִּמְלֹ֣אות שִׂ֭פְקֹו יֵ֣צֶר לֹ֑ו כָּל־יַ֖ד עָמֵ֣ל תְּבֹואֶֽנּוּ׃ | 22 |
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
יְהִ֤י ׀ לְמַלֵּ֬א בִטְנֹ֗ו יְֽשַׁלַּח־בֹּ֖ו חֲרֹ֣ון אַפֹּ֑ו וְיַמְטֵ֥ר עָ֝לֵ֗ימֹו בִּלְחוּמֹֽו׃ | 23 |
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
יִ֭בְרַח מִנֵּ֣שֶׁק בַּרְזֶ֑ל תַּ֝חְלְפֵ֗הוּ קֶ֣שֶׁת נְחוּשָֽׁה׃ | 24 |
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
שָׁלַף֮ וַיֵּצֵ֪א מִגֵּ֫וָ֥ה וּ֭בָרָק מִֽמְּרֹרָתֹ֥ו יַהֲלֹ֗ךְ עָלָ֥יו אֵמִֽים׃ | 25 |
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
כָּל־חֹשֶׁךְ֮ טָמ֪וּן לִצְפּ֫וּנָ֥יו תְּ֭אָכְלֵהוּ אֵ֣שׁ לֹֽא־נֻפָּ֑ח יֵ֖רַע שָׂרִ֣יד בְּאָהֳלֹֽו׃ | 26 |
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
יְגַלּ֣וּ שָׁמַ֣יִם עֲוֹנֹ֑ו וְ֝אֶ֗רֶץ מִתְקֹומָ֘מָ֥ה לֹֽו׃ | 27 |
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
יִ֭גֶל יְב֣וּל בֵּיתֹ֑ו נִ֝גָּרֹ֗ות בְּיֹ֣ום אַפֹּֽו׃ | 28 |
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
זֶ֤ה ׀ חֵֽלֶק־אָדָ֣ם רָ֭שָׁע מֵאֱלֹהִ֑ים וְנַחֲלַ֖ת אִמְרֹ֣ו מֵאֵֽל׃ פ | 29 |
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”