< תהילים 94 >

אל-נקמות יהוה אל נקמות הופיע 1
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
הנשא שפט הארץ השב גמול על-גאים 2
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
עד-מתי רשעים יהוה עד-מתי רשעים יעלזו 3
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
יביעו ידברו עתק יתאמרו כל-פעלי און 4
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
עמך יהוה ידכאו ונחלתך יענו 5
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
אלמנה וגר יהרגו ויתומים ירצחו 6
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
ויאמרו לא יראה-יה ולא-יבין אלהי יעקב 7
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
בינו בערים בעם וכסילים מתי תשכילו 8
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
הנטע אזן הלא ישמע אם-יצר עין הלא יביט 9
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
היסר גוים הלא יוכיח המלמד אדם דעת 10
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
יהוה--ידע מחשבות אדם כי-המה הבל 11
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
אשרי הגבר אשר-תיסרנו יה ומתורתך תלמדנו 12
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
להשקיט לו מימי רע-- עד יכרה לרשע שחת 13
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
כי לא-יטש יהוה עמו ונחלתו לא יעזב 14
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
כי-עד-צדק ישוב משפט ואחריו כל-ישרי-לב 15
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
מי-יקום לי עם-מרעים מי-יתיצב לי עם-פעלי און 16
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
לולי יהוה עזרתה לי-- כמעט שכנה דומה נפשי 17
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
אם-אמרתי מטה רגלי חסדך יהוה יסעדני 18
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
ברב שרעפי בקרבי-- תנחומיך ישעשעו נפשי 19
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
היחברך כסא הוות יצר עמל עלי-חק 20
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
יגודו על-נפש צדיק ודם נקי ירשיעו 21
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
ויהי יהוה לי למשגב ואלהי לצור מחסי 22
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
וישב עליהם את אונם-- וברעתם יצמיתם יצמיתם יהוה אלהינו 23
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< תהילים 94 >