< תהילים 92 >

מזמור שיר ליום השבת ב טוב להדות ליהוה ולזמר לשמך עליון 1
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
להגיד בבקר חסדך ואמונתך בלילות 2
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
עלי-עשור ועלי-נבל עלי הגיון בכנור 3
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
כי שמחתני יהוה בפעלך במעשי ידיך ארנן 4
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
מה-גדלו מעשיך יהוה מאד עמקו מחשבתיך 5
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
איש-בער לא ידע וכסיל לא-יבין את-זאת 6
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
בפרח רשעים כמו עשב ויציצו כל-פעלי און להשמדם עדי-עד 7
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
ואתה מרום-- לעלם יהוה 8
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
כי הנה איביך יהוה-- כי-הנה איביך יאבדו יתפרדו כל-פעלי און 9
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
ותרם כראים קרני בלתי בשמן רענן 10
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
ותבט עיני בשורי בקמים עלי מרעים-- תשמענה אזני 11
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
צדיק כתמר יפרח כארז בלבנון ישגה 12
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
שתולים בבית יהוה בחצרות אלהינו יפריחו 13
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
עוד ינובון בשיבה דשנים ורעננים יהיו 14
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
להגיד כי-ישר יהוה צורי ולא-עלתה (עולתה) בו 15
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< תהילים 92 >