< תהילים 60 >

למנצח על-שושן עדות מכתם לדוד ללמד ב בהצותו את ארם נהרים-- ואת-ארם צובה וישב יואב ויך את-אדום בגיא-מלח-- שנים עשר אלף ג אלהים זנחתנו פרצתנו אנפת תשובב לנו 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
הרעשתה ארץ פצמתה רפה שבריה כי-מטה 2
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
הראית עמך קשה השקיתנו יין תרעלה 3
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
נתתה ליראיך נס להתנוסס-- מפני קשט סלה 4
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
למען יחלצון ידידיך הושיעה ימינך ועננו (וענני) 5
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
אלהים דבר בקדשו--אעלזה אחלקה שכם ועמק סכות אמדד 6
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
לי גלעד ולי מנשה ואפרים מעוז ראשי יהודה מחקקי 7
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
מואב סיר רחצי--על-אדום אשליך נעלי עלי פלשת התרועעי 8
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
מי יבלני עיר מצור מי נחני עד-אדום 9
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
הלא-אתה אלהים זנחתנו ולא-תצא אלהים בצבאותינו 10
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
הבה-לנו עזרת מצר ושוא תשועת אדם 11
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
באלהים נעשה-חיל והוא יבוס צרינו 12
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< תהילים 60 >