< תהילים 58 >

למנצח אל-תשחת לדוד מכתם ב האמנם--אלם צדק תדברון מישרים תשפטו בני אדם 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
אף-בלב עולת תפעלון בארץ--חמס ידיכם תפלסון 2
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
זרו רשעים מרחם תעו מבטן דברי כזב 3
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
חמת-למו כדמות חמת-נחש כמו-פתן חרש יאטם אזנו 4
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
אשר לא-ישמע לקול מלחשים חובר חברים מחכם 5
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
אלהים--הרס שנימו בפימו מלתעות כפירים נתץ יהוה 6
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
ימאסו כמו-מים יתהלכו-למו ידרך חצו כמו יתמללו 7
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
כמו שבלול תמס יהלך נפל אשת בל-חזו שמש 8
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
בטרם יבינו סירתכם אטד כמו-חי כמו-חרון ישערנו 9
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
ישמח צדיק כי-חזה נקם פעמיו ירחץ בדם הרשע 10
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
ויאמר אדם אך-פרי לצדיק אך יש-אלהים שפטים בארץ 11
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< תהילים 58 >