< תהילים 22 >

למנצח על-אילת השחר מזמור לדוד ב אלי אלי למה עזבתני רחוק מישועתי דברי שאגתי 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
אלהי--אקרא יומם ולא תענה ולילה ולא-דמיה לי 2
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
ואתה קדוש-- יושב תהלות ישראל 3
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
בך בטחו אבתינו בטחו ותפלטמו 4
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
אליך זעקו ונמלטו בך בטחו ולא-בושו 5
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
ואנכי תולעת ולא-איש חרפת אדם ובזוי עם 6
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
כל-ראי ילעגו לי יפטירו בשפה יניעו ראש 7
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
גל אל-יהוה יפלטהו יצילהו כי חפץ בו 8
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
כי-אתה גחי מבטן מבטיחי על-שדי אמי 9
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
עליך השלכתי מרחם מבטן אמי אלי אתה 10
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
אל-תרחק ממני כי-צרה קרובה כי-אין עוזר 11
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
סבבוני פרים רבים אבירי בשן כתרוני 12
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
פצו עלי פיהם אריה טרף ושאג 13
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
כמים נשפכתי-- והתפרדו כל-עצמותי היה לבי כדונג נמס בתוך מעי 14
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
יבש כחרש כחי ולשוני מדבק מלקוחי ולעפר-מות תשפתני 15
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
כי סבבוני כלבים עדת מרעים הקיפוני כארי ידי ורגלי 16
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
אספר כל-עצמותי המה יביטו יראו-בי 17
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
יחלקו בגדי להם ועל-לבושי יפילו גורל 18
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
ואתה יהוה אל-תרחק אילותי לעזרתי חושה 19
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
הצילה מחרב נפשי מיד-כלב יחידתי 20
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
הושיעני מפי אריה ומקרני רמים עניתני 21
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
אספרה שמך לאחי בתוך קהל אהללך 22
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
יראי יהוה הללוהו-- כל-זרע יעקב כבדוהו וגורו ממנו כל-זרע ישראל 23
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
כי לא-בזה ולא שקץ ענות עני-- ולא-הסתיר פניו ממנו ובשועו אליו שמע 24
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
מאתך תהלתי בקהל רב--נדרי אשלם נגד יראיו 25
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
יאכלו ענוים וישבעו-- יהללו יהוה דרשיו יחי לבבכם לעד 26
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
יזכרו וישבו אל-יהוה-- כל-אפסי-ארץ וישתחוו לפניך כל-משפחות גוים 27
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
כי ליהוה המלוכה ומשל בגוים 28
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
אכלו וישתחוו כל-דשני-ארץ-- לפניו יכרעו כל-יורדי עפר ונפשו לא חיה 29
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
זרע יעבדנו יספר לאדני לדור 30
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
יבאו ויגידו צדקתו לעם נולד כי עשה 31
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< תהילים 22 >