< תהילים 2 >

למה רגשו גוים ולאמים יהגו-ריק 1
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
יתיצבו מלכי-ארץ-- ורוזנים נוסדו-יחד על-יהוה ועל-משיחו 2
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
ננתקה את-מוסרותימו ונשליכה ממנו עבתימו 3
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
יושב בשמים ישחק אדני ילעג-למו 4
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
אז ידבר אלימו באפו ובחרונו יבהלמו 5
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
ואני נסכתי מלכי על-ציון הר-קדשי 6
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
אספרה אל-חק יהוה אמר אלי בני אתה--אני היום ילדתיך 7
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
שאל ממני--ואתנה גוים נחלתך ואחזתך אפסי-ארץ 8
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
תרעם בשבט ברזל ככלי יוצר תנפצם 9
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
ועתה מלכים השכילו הוסרו שפטי ארץ 10
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
עבדו את-יהוה ביראה וגילו ברעדה 11
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
נשקו-בר פן-יאנף ותאבדו דרך-- כי-יבער כמעט אפו אשרי כל-חוסי בו 12
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< תהילים 2 >