< תהילים 2 >
למה רגשו גוים ולאמים יהגו-ריק | 1 |
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
יתיצבו מלכי-ארץ-- ורוזנים נוסדו-יחד על-יהוה ועל-משיחו | 2 |
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
ננתקה את-מוסרותימו ונשליכה ממנו עבתימו | 3 |
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
יושב בשמים ישחק אדני ילעג-למו | 4 |
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
אז ידבר אלימו באפו ובחרונו יבהלמו | 5 |
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
ואני נסכתי מלכי על-ציון הר-קדשי | 6 |
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
אספרה אל-חק יהוה אמר אלי בני אתה--אני היום ילדתיך | 7 |
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
שאל ממני--ואתנה גוים נחלתך ואחזתך אפסי-ארץ | 8 |
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
תרעם בשבט ברזל ככלי יוצר תנפצם | 9 |
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
ועתה מלכים השכילו הוסרו שפטי ארץ | 10 |
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
עבדו את-יהוה ביראה וגילו ברעדה | 11 |
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
נשקו-בר פן-יאנף ותאבדו דרך-- כי-יבער כמעט אפו אשרי כל-חוסי בו | 12 |
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.