< תהילים 122 >

שיר המעלות לדוד שמחתי באמרים לי-- בית יהוה נלך 1
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
עמדות היו רגלינו-- בשעריך ירושלם 2
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
ירושלם הבנויה-- כעיר שחברה-לה יחדו 3
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
ששם עלו שבטים שבטי-יה--עדות לישראל להדות לשם יהוה 4
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
כי שמה ישבו כסאות למשפט כסאות לבית דוד 5
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
שאלו שלום ירושלם ישליו אהביך 6
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
יהי-שלום בחילך שלוה בארמנותיך 7
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
למען אחי ורעי-- אדברה-נא שלום בך 8
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
למען בית-יהוה אלהינו-- אבקשה טוב לך 9
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< תהילים 122 >