< תהילים 114 >

בצאת ישראל ממצרים בית יעקב מעם לעז 1
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
היתה יהודה לקדשו ישראל ממשלותיו 2
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
הים ראה וינס הירדן יסב לאחור 3
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
ההרים רקדו כאילים גבעות כבני-צאן 4
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
מה-לך הים כי תנוס הירדן תסב לאחור 5
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
ההרים תרקדו כאילים גבעות כבני-צאן 6
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
מלפני אדון חולי ארץ מלפני אלוה יעקב 7
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
ההפכי הצור אגם-מים חלמיש למעינו-מים 8
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< תהילים 114 >