< תהילים 102 >

תפלה לעני כי-יעטף-- ולפני יהוה ישפך שיחו ב יהוה שמעה תפלתי ושועתי אליך תבוא 1
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
אל-תסתר פניך ממני-- ביום צר-לי הטה-אלי אזנך ביום אקרא מהר ענני 2
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
כי-כלו בעשן ימי ועצמותי כמוקד נחרו 3
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
הוכה-כעשב ויבש לבי כי-שכחתי מאכל לחמי 4
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
מקול אנחתי-- דבקה עצמי לבשרי 5
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
דמיתי לקאת מדבר הייתי ככוס חרבות 6
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
שקדתי ואהיה-- כצפור בודד על-גג 7
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
כל-היום חרפוני אויבי מהוללי בי נשבעו 8
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
כי-אפר כלחם אכלתי ושקוי בבכי מסכתי 9
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
מפני-זעמך וקצפך-- כי נשאתני ותשליכני 10
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
ימי כצל נטוי ואני כעשב איבש 11
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
ואתה יהוה לעולם תשב וזכרך לדר ודר 12
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
אתה תקום תרחם ציון כי-עת לחננה כי-בא מועד 13
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
כי-רצו עבדיך את-אבניה ואת-עפרה יחננו 14
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
וייראו גוים את-שם יהוה וכל-מלכי הארץ את-כבודך 15
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
כי-בנה יהוה ציון-- נראה בכבודו 16
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
פנה אל-תפלת הערער ולא-בזה את-תפלתם 17
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
תכתב זאת לדור אחרון ועם נברא יהלל-יה 18
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
כי-השקיף ממרום קדשו יהוה משמים אל-ארץ הביט 19
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
לשמע אנקת אסיר לפתח בני תמותה 20
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
לספר בציון שם יהוה ותהלתו בירושלם 21
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
בהקבץ עמים יחדו וממלכות לעבד את-יהוה 22
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
ענה בדרך כחו (כחי) קצר ימי 23
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
אמר--אלי אל תעלני בחצי ימי בדור דורים שנותיך 24
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
לפנים הארץ יסדת ומעשה ידיך שמים 25
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
המה יאבדו-- ואתה תעמד וכלם כבגד יבלו כלבוש תחליפם ויחלפו 26
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
ואתה-הוא ושנותיך לא יתמו 27
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
בני-עבדיך ישכונו וזרעם לפניך יכון 28
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< תהילים 102 >