< מִשְׁלֵי 8 >

הלא-חכמה תקרא ותבונה תתן קולה 1
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
בראש-מרמים עלי-דרך בית נתיבות נצבה 2
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
ליד-שערים לפי-קרת מבוא פתחים תרנה 3
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
אליכם אישים אקרא וקולי אל-בני אדם 4
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
הבינו פתאים ערמה וכסילים הבינו לב 5
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
שמעו כי-נגידים אדבר ומפתח שפתי מישרים 6
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
כי-אמת יהגה חכי ותועבת שפתי רשע 7
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
בצדק כל-אמרי-פי אין בהם נפתל ועקש 8
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
כלם נכחים למבין וישרים למצאי דעת 9
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
קחו-מוסרי ואל-כסף ודעת מחרוץ נבחר 10
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
כי-טובה חכמה מפנינים וכל-חפצים לא ישוו-בה 11
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
אני-חכמה שכנתי ערמה ודעת מזמות אמצא 12
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
יראת יהוה שנאת-רע גאה וגאון ודרך רע ופי תהפכות שנאתי 13
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
לי-עצה ותושיה אני בינה לי גבורה 14
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
בי מלכים ימלכו ורזנים יחקקו צדק 15
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
בי שרים ישרו ונדיבים כל-שפטי צדק 16
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
אני אהביה (אהבי) אהב ומשחרי ימצאנני 17
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
עשר-וכבוד אתי הון עתק וצדקה 18
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
טוב פריי מחרוץ ומפז ותבואתי מכסף נבחר 19
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
בארח-צדקה אהלך בתוך נתיבות משפט 20
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
להנחיל אהבי יש ואצרתיהם אמלא 21
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
יהוה--קנני ראשית דרכו קדם מפעליו מאז 22
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
מעולם נסכתי מראש-- מקדמי-ארץ 23
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
באין-תהמות חוללתי באין מעינות נכבדי-מים 24
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
בטרם הרים הטבעו לפני גבעות חוללתי 25
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
עד-לא עשה ארץ וחוצות וראש עפרות תבל 26
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
בהכינו שמים שם אני בחקו חוג על-פני תהום 27
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
באמצו שחקים ממעל בעזוז עינות תהום 28
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
בשומו לים חקו ומים לא יעברו-פיו בחוקו מוסדי ארץ 29
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
ואהיה אצלו אמון ואהיה שעשועים יום יום משחקת לפניו בכל-עת 30
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
משחקת בתבל ארצו ושעשעי את-בני אדם 31
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
ועתה בנים שמעו-לי ואשרי דרכי ישמרו 32
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
שמעו מוסר וחכמו ואל-תפרעו 33
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
אשרי אדם שמע-לי לשקד על-דלתתי יום יום--לשמר מזוזת פתחי 34
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
כי מצאי מצאי (מצא) חיים ויפק רצון מיהוה 35
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
וחטאי חמס נפשו כל-משנאי אהבו מות 36
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< מִשְׁלֵי 8 >