< מִשְׁלֵי 7 >

בני שמר אמרי ומצותי תצפן אתך 1
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
שמר מצותי וחיה ותורתי כאישון עיניך 2
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
קשרם על-אצבעתיך כתבם על-לוח לבך 3
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
אמר לחכמה אחתי את ומדע לבינה תקרא 4
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
לשמרך מאשה זרה מנכריה אמריה החליקה 5
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
כי בחלון ביתי-- בעד אשנבי נשקפתי 6
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
וארא בפתאים אבינה בבנים-- נער חסר-לב 7
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
עבר בשוק אצל פנה ודרך ביתה יצעד 8
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
בנשף-בערב יום באישון לילה ואפלה 9
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
והנה אשה לקראתו שית זונה ונצרת לב 10
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
המיה היא וסררת בביתה לא-ישכנו רגליה 11
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
פעם בחוץ--פעם ברחבות ואצל כל-פנה תארב 12
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
והחזיקה בו ונשקה לו העזה פניה ותאמר לו 13
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
זבחי שלמים עלי היום שלמתי נדרי 14
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
על-כן יצאתי לקראתך לשחר פניך ואמצאך 15
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
מרבדים רבדתי ערשי חטבות אטון מצרים 16
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
נפתי משכבי-- מר אהלים וקנמון 17
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
לכה נרוה דדים עד-הבקר נתעלסה באהבים 18
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
כי אין האיש בביתו הלך בדרך מרחוק 19
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
צרור-הכסף לקח בידו ליום הכסא יבא ביתו 20
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
הטתו ברב לקחה בחלק שפתיה תדיחנו 21
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
הולך אחריה פתאם כשור אל-טבח יבא וכעכס אל-מוסר אויל 22
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
עד יפלח חץ כבדו-- כמהר צפור אל-פח ולא-ידע כי-בנפשו הוא 23
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
ועתה בנים שמעו-לי והקשיבו לאמרי-פי 24
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
אל-ישט אל-דרכיה לבך אל-תתע בנתיבותיה 25
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
כי-רבים חללים הפילה ועצמים כל-הרגיה 26
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
דרכי שאול ביתה ירדות אל-חדרי-מות (Sheol h7585) 27
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)

< מִשְׁלֵי 7 >