< מִשְׁלֵי 5 >

בני לחכמתי הקשיבה לתבונתי הט-אזנך 1
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
לשמר מזמות ודעת שפתיך ינצרו 2
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
כי נפת תטפנה שפתי זרה וחלק משמן חכה 3
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
ואחריתה מרה כלענה חדה כחרב פיות 4
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
רגליה ירדות מות שאול צעדיה יתמכו (Sheol h7585) 5
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
ארח חיים פן-תפלס נעו מעגלתיה לא תדע 6
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
ועתה בנים שמעו-לי ואל-תסורו מאמרי-פי 7
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
הרחק מעליה דרכך ואל-תקרב אל-פתח ביתה 8
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
פן-תתן לאחרים הודך ושנתיך לאכזרי 9
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
פן-ישבעו זרים כחך ועצביך בבית נכרי 10
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
ונהמת באחריתך בכלות בשרך ושארך 11
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
ואמרת--איך שנאתי מוסר ותוכחת נאץ לבי 12
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
ולא-שמעתי בקול מורי ולמלמדי לא-הטיתי אזני 13
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
כמעט הייתי בכל-רע-- בתוך קהל ועדה 14
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
שתה-מים מבורך ונזלים מתוך בארך 15
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
יפוצו מעינתיך חוצה ברחבות פלגי-מים 16
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
יהיו-לך לבדך ואין לזרים אתך 17
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
יהי-מקורך ברוך ושמח מאשת נעורך 18
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
אילת אהבים ויעלת-חן דדיה ירוך בכל-עת באהבתה תשגה תמיד 19
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
ולמה תשגה בני בזרה ותחבק חק נכריה 20
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
כי נכח עיני יהוה--דרכי-איש וכל-מעגלתיו מפלס 21
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
עוונתיו--ילכדנו את-הרשע ובחבלי חטאתו יתמך 22
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
הוא--ימות באין מוסר וברב אולתו ישגה 23
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.

< מִשְׁלֵי 5 >