< איוב 33 >
ואולם--שמע-נא איוב מלי וכל-דברי האזינה | 1 |
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
הנה-נא פתחתי פי דברה לשוני בחכי | 2 |
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
ישר-לבי אמרי ודעת שפתי ברור מללו | 3 |
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
רוח-אל עשתני ונשמת שדי תחיני | 4 |
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
אם-תוכל השיבני ערכה לפני התיצבה | 5 |
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
הן-אני כפיך לאל מחמר קרצתי גם-אני | 6 |
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
הנה אמתי לא תבעתך ואכפי עליך לא-יכבד | 7 |
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
אך אמרת באזני וקול מלין אשמע | 8 |
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
זך אני בלי-פשע חף אנכי ולא עון לי | 9 |
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
הן תנואות עלי ימצא יחשבני לאויב לו | 10 |
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
ישם בסד רגלי ישמר כל-ארחתי | 11 |
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
הן-זאת לא-צדקת אענך כי-ירבה אלוה מאנוש | 12 |
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
מדוע אליו ריבות כי כל-דבריו לא יענה | 13 |
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
כי-באחת ידבר-אל ובשתים לא ישורנה | 14 |
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
בחלום חזיון לילה--בנפל תרדמה על-אנשים בתנומות עלי משכב | 15 |
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
אז יגלה אזן אנשים ובמסרם יחתם | 16 |
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
להסיר אדם מעשה וגוה מגבר יכסה | 17 |
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
יחשך נפשו מני-שחת וחיתו מעבר בשלח | 18 |
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
והוכח במכאוב על-משכבו וריב (ורוב) עצמיו אתן | 19 |
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
וזהמתו חיתו לחם ונפשו מאכל תאוה | 20 |
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
יכל בשרו מראי ושפי (ושפו) עצמתיו לא ראו | 21 |
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
ותקרב לשחת נפשו וחיתו לממתים | 22 |
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
אם-יש עליו מלאך--מליץ אחד מני-אלף להגיד לאדם ישרו | 23 |
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
ויחננו--ויאמר פדעהו מרדת שחת מצאתי כפר | 24 |
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
רטפש בשרו מנער ישוב לימי עלומיו | 25 |
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
יעתר אל-אלוה וירצהו וירא פניו בתרועה וישב לאנוש צדקתו | 26 |
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
ישר על-אנשים ויאמר חטאתי וישר העויתי ולא-שוה לי | 27 |
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
פדה נפשי (נפשו) מעבר בשחת וחיתי (וחיתו) באור תראה | 28 |
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
הן-כל-אלה יפעל-אל-- פעמים שלוש עם-גבר | 29 |
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
להשיב נפשו מני-שחת-- לאור באור החיים | 30 |
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
הקשב איוב שמע-לי החרש ואנכי אדבר | 31 |
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
אם-יש-מלין השיבני דבר כי-חפצתי צדקך | 32 |
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
אם-אין אתה שמע-לי החרש ואאלפך חכמה | 33 |
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”