< איוב 22 >

ויען אליפז התמני ויאמר 1
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
הלאל יסכן-גבר-- כי-יסכן עלימו משכיל 2
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
החפץ לשדי כי תצדק ואם-בצע כי-תתם דרכיך 3
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
המיראתך יכיחך יבוא עמך במשפט 4
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
הלא רעתך רבה ואין-קץ לעונתיך 5
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
כי-תחבל אחיך חנם ובגדי ערומים תפשיט 6
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
לא-מים עיף תשקה ומרעב תמנע-לחם 7
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
ואיש זרוע לו הארץ ונשוא פנים ישב בה 8
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
אלמנות שלחת ריקם וזרעות יתמים ידכא 9
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
על-כן סביבותיך פחים ויבהלך פחד פתאם 10
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
או-חשך לא-תראה ושפעת-מים תכסך 11
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
הלא-אלוה גבה שמים וראה ראש כוכבים כי-רמו 12
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
ואמרת מה-ידע אל הבעד ערפל ישפוט 13
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
עבים סתר-לו ולא יראה וחוג שמים יתהלך 14
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
הארח עולם תשמור-- אשר דרכו מתי-און 15
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
אשר-קמטו ולא-עת נהר יוצק יסודם 16
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
האמרים לאל סור ממנו ומה-יפעל שדי למו 17
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
והוא מלא בתיהם טוב ועצת רשעים רחקה מני 18
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
יראו צדיקים וישמחו ונקי ילעג-למו 19
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
אם-לא נכחד קימנו ויתרם אכלה אש 20
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
הסכן-נא עמו ושלם בהם תבואתך טובה 21
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
קח-נא מפיו תורה ושים אמריו בלבבך 22
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
אם-תשוב עד-שדי תבנה תרחיק עולה מאהלך 23
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
ושית-על-עפר בצר ובצור נחלים אופיר 24
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
והיה שדי בצריך וכסף תועפות לך 25
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
כי-אז על-שדי תתענג ותשא אל-אלוה פניך 26
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
תעתיר אליו וישמעך ונדריך תשלם 27
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
ותגזר-אמר ויקם לך ועל-דרכיך נגה אור 28
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
כי-השפילו ותאמר גוה ושח עינים יושע 29
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
ימלט אי-נקי ונמלט בבר כפיך 30
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< איוב 22 >