< איוב 22 >
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
הלאל יסכן-גבר-- כי-יסכן עלימו משכיל | 2 |
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
החפץ לשדי כי תצדק ואם-בצע כי-תתם דרכיך | 3 |
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
המיראתך יכיחך יבוא עמך במשפט | 4 |
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
הלא רעתך רבה ואין-קץ לעונתיך | 5 |
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
כי-תחבל אחיך חנם ובגדי ערומים תפשיט | 6 |
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
לא-מים עיף תשקה ומרעב תמנע-לחם | 7 |
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
ואיש זרוע לו הארץ ונשוא פנים ישב בה | 8 |
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
אלמנות שלחת ריקם וזרעות יתמים ידכא | 9 |
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
על-כן סביבותיך פחים ויבהלך פחד פתאם | 10 |
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
או-חשך לא-תראה ושפעת-מים תכסך | 11 |
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
הלא-אלוה גבה שמים וראה ראש כוכבים כי-רמו | 12 |
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
ואמרת מה-ידע אל הבעד ערפל ישפוט | 13 |
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
עבים סתר-לו ולא יראה וחוג שמים יתהלך | 14 |
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
הארח עולם תשמור-- אשר דרכו מתי-און | 15 |
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
אשר-קמטו ולא-עת נהר יוצק יסודם | 16 |
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
האמרים לאל סור ממנו ומה-יפעל שדי למו | 17 |
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
והוא מלא בתיהם טוב ועצת רשעים רחקה מני | 18 |
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
יראו צדיקים וישמחו ונקי ילעג-למו | 19 |
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
אם-לא נכחד קימנו ויתרם אכלה אש | 20 |
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
הסכן-נא עמו ושלם בהם תבואתך טובה | 21 |
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
קח-נא מפיו תורה ושים אמריו בלבבך | 22 |
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
אם-תשוב עד-שדי תבנה תרחיק עולה מאהלך | 23 |
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
ושית-על-עפר בצר ובצור נחלים אופיר | 24 |
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
והיה שדי בצריך וכסף תועפות לך | 25 |
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
כי-אז על-שדי תתענג ותשא אל-אלוה פניך | 26 |
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
תעתיר אליו וישמעך ונדריך תשלם | 27 |
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
ותגזר-אמר ויקם לך ועל-דרכיך נגה אור | 28 |
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
כי-השפילו ותאמר גוה ושח עינים יושע | 29 |
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
ימלט אי-נקי ונמלט בבר כפיך | 30 |
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”