< איוב 21 >

ויען איוב ויאמר 1
Sai Ayuba ya amsa,
שמעו שמוע מלתי ותהי-זאת תנחומתיכם 2
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
שאוני ואנכי אדבר ואחר דברי תלעיג 3
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
האנכי לאדם שיחי ואם-מדוע לא-תקצר רוחי 4
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
פנו-אלי והשמו ושימו יד על-פה 5
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
ואם-זכרתי ונבהלתי ואחז בשרי פלצות 6
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
מדוע רשעים יחיו עתקו גם-גברו חיל 7
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
זרעם נכון לפניהם עמם וצאצאיהם לעיניהם 8
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
בתיהם שלום מפחד ולא שבט אלוה עליהם 9
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
שורו עבר ולא יגעל תפלט פרתו ולא תשכל 10
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
ישלחו כצאן עויליהם וילדיהם ירקדון 11
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
ישאו כתף וכנור וישמחו לקול עוגב 12
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
יבלו (יכלו) בטוב ימיהם וברגע שאול יחתו (Sheol h7585) 13
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
ויאמרו לאל סור ממנו ודעת דרכיך לא חפצנו 14
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
מה-שדי כי-נעבדנו ומה-נועיל כי נפגע-בו 15
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
הן לא בידם טובם עצת רשעים רחקה מני 16
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
כמה נר-רשעים ידעך-- ויבא עלימו אידם חבלים יחלק באפו 17
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
יהיו כתבן לפני-רוח וכמץ גנבתו סופה 18
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
אלוה יצפן-לבניו אונו ישלם אליו וידע 19
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
יראו עינו כידו ומחמת שדי ישתה 20
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
כי מה-חפצו בביתו אחריו ומספר חדשיו חצצו 21
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
הלאל ילמד-דעת והוא רמים ישפוט 22
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
זה--ימות בעצם תמו כלו שלאנן ושליו 23
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
עטיניו מלאו חלב ומח עצמותיו ישקה 24
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
וזה--ימות בנפש מרה ולא-אכל בטובה 25
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
יחד על-עפר ישכבו ורמה תכסה עליהם 26
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
הן ידעתי מחשבותיכם ומזמות עלי תחמסו 27
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
כי תאמרו איה בית-נדיב ואיה אהל משכנות רשעים 28
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
הלא שאלתם עוברי דרך ואתתם לא תנכרו 29
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
כי ליום איד יחשך רע ליום עברות יובלו 30
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
מי-יגיד על-פניו דרכו והוא-עשה מי ישלם-לו 31
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
והוא לקברות יובל ועל-גדיש ישקוד 32
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
מתקו-לו רגבי-נחל ואחריו כל-אדם ימשוך ולפניו אין מספר 33
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
ואיך תנחמוני הבל ותשובתיכם נשאר-מעל 34
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< איוב 21 >