< איוב 21 >
שמעו שמוע מלתי ותהי-זאת תנחומתיכם | 2 |
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
שאוני ואנכי אדבר ואחר דברי תלעיג | 3 |
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
האנכי לאדם שיחי ואם-מדוע לא-תקצר רוחי | 4 |
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
פנו-אלי והשמו ושימו יד על-פה | 5 |
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
ואם-זכרתי ונבהלתי ואחז בשרי פלצות | 6 |
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
מדוע רשעים יחיו עתקו גם-גברו חיל | 7 |
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
זרעם נכון לפניהם עמם וצאצאיהם לעיניהם | 8 |
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
בתיהם שלום מפחד ולא שבט אלוה עליהם | 9 |
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
שורו עבר ולא יגעל תפלט פרתו ולא תשכל | 10 |
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
ישלחו כצאן עויליהם וילדיהם ירקדון | 11 |
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
ישאו כתף וכנור וישמחו לקול עוגב | 12 |
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
יבלו (יכלו) בטוב ימיהם וברגע שאול יחתו (Sheol ) | 13 |
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
ויאמרו לאל סור ממנו ודעת דרכיך לא חפצנו | 14 |
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
מה-שדי כי-נעבדנו ומה-נועיל כי נפגע-בו | 15 |
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
הן לא בידם טובם עצת רשעים רחקה מני | 16 |
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
כמה נר-רשעים ידעך-- ויבא עלימו אידם חבלים יחלק באפו | 17 |
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
יהיו כתבן לפני-רוח וכמץ גנבתו סופה | 18 |
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
אלוה יצפן-לבניו אונו ישלם אליו וידע | 19 |
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
יראו עינו כידו ומחמת שדי ישתה | 20 |
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
כי מה-חפצו בביתו אחריו ומספר חדשיו חצצו | 21 |
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
הלאל ילמד-דעת והוא רמים ישפוט | 22 |
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
זה--ימות בעצם תמו כלו שלאנן ושליו | 23 |
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
עטיניו מלאו חלב ומח עצמותיו ישקה | 24 |
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
וזה--ימות בנפש מרה ולא-אכל בטובה | 25 |
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
יחד על-עפר ישכבו ורמה תכסה עליהם | 26 |
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
הן ידעתי מחשבותיכם ומזמות עלי תחמסו | 27 |
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
כי תאמרו איה בית-נדיב ואיה אהל משכנות רשעים | 28 |
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
הלא שאלתם עוברי דרך ואתתם לא תנכרו | 29 |
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
כי ליום איד יחשך רע ליום עברות יובלו | 30 |
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
מי-יגיד על-פניו דרכו והוא-עשה מי ישלם-לו | 31 |
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
והוא לקברות יובל ועל-גדיש ישקוד | 32 |
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
מתקו-לו רגבי-נחל ואחריו כל-אדם ימשוך ולפניו אין מספר | 33 |
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
ואיך תנחמוני הבל ותשובתיכם נשאר-מעל | 34 |
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”